• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 1, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Hadiza Gabon a kotu: Rayuwa ta ta na cikin haɗari

by DAGA IRO MAMMAN
August 1, 2022
in Labarai
0
Hadiza Aliyu Gabon

Hadiza Aliyu Gabon

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCIYAR jarumar Kannywood Hadiza Gabon ta bayyana cewa shari’ar da ake tafkawa da ita a Kaduna ta jefa rayuwar ta cikin haɗari.

Ta faɗi haka ne a gaban alƙalin kotun Shari’ar Musulunci da ke Magajin Gari, Kaduna, a yau Litinin a cigaba da sauraren ƙarar ta da wani mutum ya kai ta.

Idan kun tuna, mujallar Fim ta ba ku labarin yadda wani ma’aikacin gwamnati mai suna Bala Musa ya maka ta a kotun bisa zargin cewa ta ci masa kuɗi har N396,000 sannan ta ƙi auren sa.

Jarumar, wadda ke zama a Kaduna, ta faɗa wa kotun a zaman da aka yi a baya cewa wannan magana dai zuƙi ta malle ce, domin ita ba ta ma san mutumin ba.

Alƙalin ya ɗage sauraron ƙarar daga ranar 28 ga Yuni, 2022, zuwa yau, 1 ga Agusta, saboda rashin lafiyar matar sa.

A yau ne aka ba Musa damar ya kawo shaidun da ya ce ya na da su.

Sai dai Hadiza Gabon ta shaida wa kotun, ta bakin lauyan ta, Barista Mubarak Sani Jibril, cewa taɓarɓarewar tsaro a ƙasar nan ya sa jarumar ta na jin tsoron zuwa kotun.

Ya ce jarumar ta na tsoron yadda a duk ranar da aka dawo kotu domin cigaba da sauraron ƙarar sai an yi dabarar ficewa da ita daga kotun.

Lauyan ya ce: “Tsaron lafiya ta ya na da muhimmanci, ita ma tsaron lafiyar ta ya na da muhimmanci, sannan tsaron lafiyar sauran jama’a ma ya na da muhimmanci a kotun, har ma da shi mai ƙarar.

“Rayuwa ta ta na cikin haɗari, rayuwar ta ta na cikin haɗari, rayuwar shi ma mai ƙarar ta na cikin haɗari. Ba mu san waye ke bibiyar shari’ar a soshiyal midiya ba. Abu na gaba shi ne za ka fara ganin ‘yan bindiga a nan sun zo satar mutane domin garkuwa da su. Wannan shi ne abin da ya dame mu, ba shari’ar da ake yi a kotu ba.”

Lauyan ya yi kira ga alƙalin da ya yi la’akari da tsaron lafiyar wadda ake ƙara ya ba ta damar ta daina zuwa kotun domin cigaba da sauraron ƙarar.

Da jin haka, sai lauyan mai ƙara, wato Barista Naira Murtala, ya ƙi amincewa da wannan roƙon, ya ce tilas ne wadda ake ƙarar ta zo kotu a ko yaushe.

A kan batun tsaron lafiyar wadda ake ƙarar kuwa, ya ce ba zai ƙi amincewa da roƙon da su ka yi ba saboda da gaske ne babu tsaro ga kowa a ƙasar, to amma akwai buƙatar su kawo shi a rubuce domin ya duba ya yi nazari.

Alƙalin kotun, Khadi Rilwanu Kyaudai, ya ba su tabbacin cewa kotun za ta duba batun tsaron lafiyar masu shari’ar a zaman kotun na gaba.

Loading

Tags: Bala MusaBarista Mubarak Sani JibrilBarista Naira MurtalaHadiza GabonKhadiKhadi Rilwanu KyaudailauyaMagajin Garirashin tsaroshari'a.
Previous Post

Gidan yanar kallon finafinan Hausa, Kallo.ng, ya samu karramawa ta duniya

Next Post

Mun sauya ofis ne saboda kiyaye mutuncin Kannywood – Alhasan Kwalle

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Malam Alhassan Kwalle

Mun sauya ofis ne saboda kiyaye mutuncin Kannywood - Alhasan Kwalle

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!