ƊAN takarar zama sanatan Kaduna ta Tsakiya a jam’iyyar APC, Muhammad Sani Abdullahi (Dattijo), ya bayyana irin gudunmawar da zai ba manishaɗanta, musamman na Kaduna da ake kira Kadawood in Allah ya ba shi nasarar cin zaɓe na 2023.
A shekaranjiya Laraba, 26 ga Oktoba, 2022, Dattijo ya yi bikin cikar sa shekara 43 a duniya, wanda aka yi a ɗakin taro na ‘Ahmed Musa Neibourhood Centre’ da ke Sabon Hanya, Kaduna.
A yayin da ya ke amsa tambaya kan abin da zai yi wa masu harkar nishaɗi idan ya samu nasara, ɗan siyasar ya ce ya ji daɗin wannan tambaya, sannan ya ƙara da cewa kamar shekara biyar da ta wuce Gwamnatin Tarayya na ba da tallafin kuɗi ga masu harkar nishaɗantarwa, amma ‘yan Kudu kaɗai ke amfana.
Ya ce: “Idan Allah ya ba mu nasara, za mu yi iyakacin bakin ƙoƙarin mu don ganin an samu damar amfana da irin wannan kuɗaɗe da ake bayarwa, musamman ‘yan Kadawood.”
Da jin haka, nan da nan ɗakin taron ya cika da sowa.
Tun farko dai ƙungiyar Kadawood sun samu gayyata ta musamman ne daga jaruma Asabe Madaki, wadda ta na daga cikin waɗanda su ka shirya bikin.
Nura MC, wanda shi ne shugaban Kadawood, shi ne ya jagoranci tawagar ‘yan fim zuwa wurin taron.
Bayan jawabai da abokan Dattijo su ka yi na taya shi murna, an kira ‘yan Kadawood don su ma su tofa albarkacin bakin su.
A daidai wannan lokacin sai Aƙilu Muhammad (Baban Mulika) ya yi wa Dattijo kirari cikin barkwanci a yadda ya ke shiri a matsayin Bayarabe.

Bayan ya gama kuma sai Sani Ɗangwari ya amsa, inda ya zaro N2,000 ‘yan ɗari biyar-biyar ya ce wa Dattijo ga su gudunmawa ne, da ma da su ka je Kano Asiwaju ya ce su riƙa ba da gudunmawa. Bayan Dattijo ya amshi kuɗin sai Ɗangwari ya sauka daga dandamalin da abin magana a hannun sa ya ce wa mahalarta taron duk mai ƙaunar Dattijo ya zo ya biya shi kuɗin shi da ya ba Dattijo.
Nan da nan kuwa ɗakin ya cika da ihu. Kan ka ce kwabo jama’a su ka yi ta zuba wa Ɗangwari da Moɗa kuɗi.
Wannan abu ya nishaɗantar da jama’a matuƙa. Shi kan shi Dattijo ya nishaɗantu, inda ya yi alƙawarin zai ba da lokacin da zai zauna da su don tattauna abubuwa muhimmai.
Daga nan ‘yan fim ɗin su ka yi masa godiya da sallama su ka watse.
Waɗanda su ka halarci taron sun haɗa da Sani Idris Kauru (Moɗa), Aƙilu Mohammed (Baban Mulika), Baba Gwanki, A.S. Muhammed, Ibrahim Usman Muhammad (Al-Imash), Ibrahim Yalawa, Nura MC, Jamil Nafseen, Zaharaddin Mando, A.A. Rasheed Kabala, Nas M. Shareef, A’ishatu Umar Mahuta, A’isha NTA, Farida Mansur, Fauziyya Yola, Nafisa Little, da Fati Wuff.

