Hukumar Gudanarwa ta gidan talbijin na Hijrah ta tabbatar da naɗin Ghali El-Abdallah DZ a matsayin sabon Manajan Darakta na tashar.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da hukumar gidan talbijin ɗin ta raba wa manema labarai, inda ta ce sun yi naɗin ne saboda irin gwagwarmayar da Ghali ya yi a gidajen rediyo da dama da kuma masana’antar Kannywood.
Ta ce wannan dalilin ya sa suka tabbatar da yana muhimmiyar gudunmawa da zai bai wa tashar Hijrah TV a irin wannan lokaci.
Ghali dai fitaccen mawaƙi ne, furodusa kuma jarumi.
An haife shi a unguwar Durumin Zungura da ke cikin birnin Kano a shekarar 1978. Ya yi makarantar firamare a Kwalli kuma ya yi Ƙaramar Sakandare a Sabuwar Ƙofa, sai Babbar Sakandare a Kwalejin Rumfa, Kano.
Ya ci gaba a Kwalejin Sa’adatu Rimi inda ya yi NCE, sai kuma ya tafi Jami’ar Bayero inda ya samu Babbar Difloma a fannin aikin jarida.
A ɓangaren aiki kuwa, Ghali ya yi aiki a gidan rediyon Freedom FM da gidan rediyon Rahama FM da gidan rediyon Arewa, sai Kannywood Series TV da kuma Hijira TV.
A Kannywood kuma Ghali ya kasance komai da ruwan ka, inda ya fara da waƙoƙin tallace-tallace da na wayar da kai. Sai kuma shirin sa mai farin jini na “Dandalin Fasaha” inda yake hira da mawaƙa da ‘yan fim.
Bugu da ƙari shi ne marubuci kuma jagoran shirya wasan kwaikwayo na ‘Birnin Dala’ a Dala FM, sai kuma wasan kwaikwayo na ‘Ƙasar Jallaba’ a tashar Arewa FM wadda daga baya aka yi fim ɗin wasan kwaikwayon da sunan ‘Mai Martaba’, fim ɗin da ya shiga jerin finafinan da suka wakilci Nijeriya a gasar Oscars a Amurka.
![]()







