• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Hukumar Tace Finafinai na samun cigaba a ƙarƙashin El-Mustapha, inji Sarkin Kano

by DAGA ABBA MUHAMMAD
November 16, 2023
in Labarai
0
Sarkin Kano tare da Abba El-Mustapha a lokacin ziyarar

Sarkin Kano tare da Abba El-Mustapha a lokacin ziyarar

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MAI Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bayyana cewa Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano ta na samun cigaba a ƙarƙashin sabon Babban Sakataren ta, Alhaji Abba El-Mustapha.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Malam Abdullahi Sani Sulaiman, ya ce sarkin ya faɗi haka ne a lokacin da shugaban hukumar ya jagoranci tawaga daga hukumar sa su ka kai wa sarkin ziyarar ban-girma a fadar sa a jiya Laraba.

Ya ce a lokacin ziyarar, sarki ya yaba wa cigaban da aka samu a hukumar a ƙarƙashin shugabancin El-Mustapha, wanda sarkin ya bayyana shi a matsayin haziƙi kuma jajirtacce, mai son kawo wa al’ummar Jihar Kano cigaba.

Haka kuma sarkin ya gode wa Gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf dangane da dogon nazari da ya yi lokacin da ya zaɓo El-Mustapha a matsayin sabon shugaban hukumar. 

Mai Martaba Sarki tare da tawagar maziyartan daga Hukumar Tace Finafinai

Ya kuma bayyana ƙarfin gwiwar sa tare da cewa tun lokacin da aka ayyana sunan Abban a matsayin wanda zai jagoranci hukumar al’ummar sa da dama ke nuna gamsuwar su da cewa lallai an ɗora ƙwarya a gurbin ta.

Sarkin ya ba hukumar tabbacin cewa ƙofar su za ta ci gaba da zama a buɗe a ko da yaushe domin shawara ko gudunmawa.

A nasa ɓangaren, El-Mustapha ya bayyana wa sarki cewa ya kai masa ziyara ne domin girmamawa tare da neman albarka ta yadda zai cimma nasarar da hukumar ta sa a gaba.

Ya kuma yi wa sarkin addu’ar Allah ya ja zamanin sa, ya ƙara masa nisan kwana.

El-Mustapha da tawagar sa a fadar Kano

Loading

Previous Post

Aiki sai mai shi: Ayyukan raya jiha da inganta rayuwar jama’a fiye da 300 a Kasafin 2024 na gwamnatin Namadi a Jigawa

Next Post

Editan finafinai a Kannywood, Hafiz SB zai yi bankwana da kwanan shago

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Hafiz Hamisu da katin gayyatar auren sa

Editan finafinai a Kannywood, Hafiz SB zai yi bankwana da kwanan shago

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!