MAI Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bayyana cewa Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano ta na samun cigaba a ƙarƙashin sabon Babban Sakataren ta, Alhaji Abba El-Mustapha.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Malam Abdullahi Sani Sulaiman, ya ce sarkin ya faɗi haka ne a lokacin da shugaban hukumar ya jagoranci tawaga daga hukumar sa su ka kai wa sarkin ziyarar ban-girma a fadar sa a jiya Laraba.
Ya ce a lokacin ziyarar, sarki ya yaba wa cigaban da aka samu a hukumar a ƙarƙashin shugabancin El-Mustapha, wanda sarkin ya bayyana shi a matsayin haziƙi kuma jajirtacce, mai son kawo wa al’ummar Jihar Kano cigaba.
Haka kuma sarkin ya gode wa Gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf dangane da dogon nazari da ya yi lokacin da ya zaɓo El-Mustapha a matsayin sabon shugaban hukumar.

Ya kuma bayyana ƙarfin gwiwar sa tare da cewa tun lokacin da aka ayyana sunan Abban a matsayin wanda zai jagoranci hukumar al’ummar sa da dama ke nuna gamsuwar su da cewa lallai an ɗora ƙwarya a gurbin ta.
Sarkin ya ba hukumar tabbacin cewa ƙofar su za ta ci gaba da zama a buɗe a ko da yaushe domin shawara ko gudunmawa.
A nasa ɓangaren, El-Mustapha ya bayyana wa sarki cewa ya kai masa ziyara ne domin girmamawa tare da neman albarka ta yadda zai cimma nasarar da hukumar ta sa a gaba.
Ya kuma yi wa sarkin addu’ar Allah ya ja zamanin sa, ya ƙara masa nisan kwana.
