FITACCIYAR jaruma Fati S.U. Garba a yau ta bayyana irin kewar mahaifiyar ta da ta ke yi tun bayan rasuwar ta shekara ɗaya da ta gabata.
A yau Lahadi, 18 ga Satumba, 2022 mahaifiyar ta cika shekara ɗaya cif da rasuwa.
Fati ta yi rubutu da Turanci da Hausa a Instagram, ta ce, “Today marks a year without you mother. Every time I smile, every time I sigh, I think of your face, and a tear escapes my eye.
“You were my world, my inspiration and my heart, my everything. I will always be that girl you were proud of Insha Allah. Allah ya saka maki da gidan Aljannah. Pls put my mother in ur prayers thank you.”
Mujallar Fim ta fassara kalamin nata kamar haka: “Yau ne shekara ɗaya daidai ba tare da ke ba Mama. Kowane lokaci ina murmushi, kowane lokaci ina ajiyar zuciya, ina tunanin fuskar ki, sai kuma hawaye ya kuɓuce a ido na.
“Ke ce duniya ta, ke ce abar tunani na kuma zuciya ta, ke ce komai nawa. Zan kasance wannan yarinyar nan dai wadda ki ke alfahari da ita Insha Allah. Allah ya saka miki da gidan Aljanna. Don Allah ku sa mahaifiya ta a cikin addu’o’in ku. Na gode.”
A bara, mujallar Fim ta ba ku labarin rasuwar mahaifiyar jarumar, wato Hajiya Hauwa S.U. Garba, da misalin ƙarfe 6:00 na safe a ranar Asabar, 18 ga Satumba, 2021, a wani asibitin kuɗi da ke Minna, Jihar Neja, bayan doguwar jinya.
Allah ya rahamshe ta, amin.