ALLAH ya azurta jarumi a Kannywood, Malam Aminu Mirror, da ƙaruwar ‘ya mace.
Maiɗakin sa, Malama Zulaihat, ta haihu da misalin ƙarfe 9:30 na daren jiya Litinin, 23 ga Janairu, 2023 a gidan sa mai lamba 261 da ke Zariya City, Jihar Kaduna.
Za a yi bikin raɗin suna a ranar Litinin mai zuwa.
Jarumin, wanda furodusa ne kuma darakta, ya shaida wa mujallar Fim cewa a yanzu ‘ya’yan sa 12 – maza bakwai, mata biyar.
Aminu Mirror sanannen mai shirya fim ne a Jihar Kaduna. Shi ne kuma mamallakin kamfanin shirya finafinai mai suna Mirror of the Moment da ke Zariya.
Yanzu haka tauraruwar sa na tashe a shirin ‘Gidan Badamasi’ mai dogon zango wanda tashar talbijin ta Arewa 24 ke nunawa, inda ya ke fitowa da sunan Malam Zaidu, sunan da masu kallo su ke kiran sa da shi.