ƁARAYI masu garkuwa da mutane, wato ‘yan kidinafin, sun sace Hajiya Halima Adamu, mahaifiyar fitaccen mawaƙi Dauda Abdullahi Kahutu (Rarara).
Majiyar mujallar Fim ta ce sun ɗauke ta ne a gidan su da ke garin Kahutu a Ƙaramar Hukumar Ɗanja da ke cikin Jihar Katsina.
Majiyar ta ƙara da cewa ɓarayin sun kutsa kai cikin gidan da misalin ƙarfe 1 na daren jiya, su ka yi awon gaba da dattijuwar.
Majiyar ta ce: “Ɓarayin sun zo ne a ƙafa ba tare da wata hayaniya ba, domin kuwa ba su yi harbi ko ɗaya ba, kuma su ka gama komai cikin mintina ƙalilan. Tsohuwar ba ta yi wata gardama ba lokacin da su ka ce mata ta tashi su tafi.
“Duk da yake ɓarayin sun samu wasu mutanen a gidan, sai su ka ɗauki mahaifiyar Rarara ita kaɗai.
“Ba a yi ƙoƙarin tare su a gidan ba saboda su na ɗauke da bindigogi.
“Watakila sun ɓoye baburan su a nesa sannan su ka taka da ƙafa zuwa cikin gari.
“Mu na addu’ar za a dawo mana da ita lafiya ƙalau domin ta na taimakon mu sosai a garin nan.
“Ɗan ta Rarara ma ya na taimaka mana ƙwarai da gaske. Ya kawo cigaba mai yawa a nan garin don jin daɗin mu.”
Mujallar Fim ta yi ƙoƙarin jin ta bakin Rarara amma hakan bai samu ba saboda layin wayar sa na kashe.