• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 1, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

KILAF 2022: Ƙasashe takwas za su kara a gasar finafinan Afrika a Kano

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
October 17, 2022
in Labarai
0
Alhaji Abdulkareem Muhammad

Alhaji Abdulkareem Muhammad

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘASASHE takwas ne, ciki har da Nijeriya, za su fafata a gasar baje-kolin finafinan harsunan Afrika ta Kano, wato ‘Kano Indigenous Languages of Africa Film Market and Festival’ (KILAF), ta bana.

An samu sama da finafinai 65 da su ka shiga gasar, waɗanda a cikin su an samu bakwai daga ƙasar waje.

Shugaban kwamitin gudanarwa na gasar, wadda ake shiryawa a duk shekara, Malam Abdulkareem Muhammad, shi ne ya faɗa wa mujallar Fim haka a lokacin da ya ke ƙarin bayani kan cikar wa’adin da aka ɗauka na shiga gasar.

Wa’adin dai ya cika ne a ranar Juma’a, 14 ga Oktoba, wanda ya sa duk wanda bai shiga ba daga ranar, to lokaci ya ƙure masa, sai dai ya jira shekara mai zuwa.

Abdulkareem ya ce, “Da man mun shirya za a rufe karɓar finafinan ne a ranar 14 ga wata, kuma alhamdu lillah ranar ta zo. An samu nasarori sosai wajen shigar da finafinai fiye da shekarun baya.”

Ya ƙara da cewa: “A baya finafinan da mu ke samu ba su da yawa, musamman daga ƙasashen waje, amma a wannan shekarar mun samu finafinai da su ka shiga daga ƙasashe bakwai kuma da yaruka daban-daban na Afirka.”

Da ya ke magana kan yawan finafinan da su ka shiga, Abdulkareem ya ce, “Finafinan da su ka shiga gasar za su kai 65 ko ma dai su wuce haka, don haka ne ma na faɗa maka gasar wannan shekarar ta fi ta baya.”

Fostar taron KILAF na bana

Ya ce za a yi tsare-tsaren da aka saba yi, kamar haska fim a sinima da za a yi a Ado Bayero Mall da bikin nuna al’adun Afirka.

Bugu da ƙari, shugaban ya bayyana cewa a bana sun gayyato ministan al’adu na ƙasar Nijar kuma ya amsa masu da cewar zai halarci bikin.

“Mu na fatan samun haɗin kai na masu kishin yaruka da kuma al’adun ƙasashen mu na Afrika,” inji shi.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa an tsayar da ranakun 22 zuwa 27 ga Nuwamba na taron, kuma ranar 26 ne za a yi gagarumin taron karramawa.

Wannan taron na bana dai shi ne karo na biyar da za a yi daga lokacin da aka fara shi.

Loading

Tags: Abdulkareem Muhammadbaje-kolicikar wa'adigasar finafinai ta Afirkaharsunan gadoKanoKano Indigenous Languages of Africa Film Market and FestivalKILAP 2022ƙasasheministan al'aduNijar
Previous Post

Ambaliya: Gwamnati ta fara kai agajin tan 12,000 na abinci a Anambra, Jigawa da wasu jihohin

Next Post

Dillalan waƙa ne ke kassara mawaƙa – Albashir Hamza Yarima

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Albashir Hamza Yareema

Dillalan waƙa ne ke kassara mawaƙa - Albashir Hamza Yarima

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!