• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Kwamishinan Shari’a ya raba faɗan hukumomi a Kano

by DAGA ABBA MUHAMMAD
August 25, 2023
in Labarai
0
Kwamishinan Shari'a (a tsakiya) ya na sasanta shugabannin hukumomin

Kwamishinan Shari'a (a tsakiya) ya na sasanta shugabannin hukumomin

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

KWAMISHINAN Shari’a na Jihar Kano, Barista Haruna Isah Dederi, ya sulhunta wani saɓani tsakanin Kwamishinar Raya Al’adu da Yawon Buɗe Ido ta jihar, Hajiya Ladidi Garko, da  Manajan Daraktan Hukumar Kula da Masu Yawon Buɗe Ido, Alhaji Tukur Bala Sagagi, tare  da Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta jihar, Alhaji Abba  El-Mustapha.

An yi taron sasantawar a babban ɗakin taro na Ma’aikatar Shari’a a Kano.

Haka kuma, an shirya taron ne domin nemo bakin zaren  rashin fahimtar da ke faruwa wajen gudanar da ayyukan da ya rataya a  tsakanin hukumomin biyu a kan masu sana’ar gidajen kallo (viewing centres) da masu gidajen shirya tarurruka (event centres). 

Da farko Dederi ya yi dogon jawabi dangane da haƙƙi tare da ayyukan da su ka rataya a kan hukumomin biyu, inda bayan doguwar tattaunawa tsakanin shugabannin hukumomin biyu aka samu daidaito.

A sama: Abba El-Mustapha tare da Barista Haruna Isa Dederi. A ƙasa kuma shi ne tare da Hajiya Ladidi Garko

El-Mustapha ya ba da shawarar a raba ayyukan gida biyu, inda kowace hukuma za ta ɗauki ɗaya don ta mai da hankali a kan sa, ita kuma Hajiya Ladidi ta yi na’am da wannan shawarar. 

Bisa la’akari da hakan, sai Dederi ya tabbatar da ba wa kowace hukuma aiki ɗaya don ta mai da hankali a kai don cimma nasarar da gwamnati ta sa a gaba.

A yanzu dai Hukumar Tace Finafinan da Ɗab’i ce ke da alhakin kula da ayyukan masu sana’ar gidajen kallo, ita kuma Hukumar Kula da Al’adu da Masu Yawon Buɗe Ido  ke da alhakin kula da ayyukan masu gidajen shirya tarurruka.

Mahalartan taron bayan an gama taron

Shugabannin sun nuna farin cikin su dangane da yadda Ma’aikatar Shari’a ta kawo ƙarshen taƙaddamar tare da samun nasarar da taron ya samu na cimma matsaya.

Loading

Previous Post

Jarumin Kannywood Jamilu Ibrahim ya samu haihuwa ta 5, jaruma Asma’u Sani ta samu ƙarin jika

Next Post

Sabunta rajista: Za mu kauce wa matsalolin baya – Gidan Dabino

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON

Sabunta rajista: Za mu kauce wa matsalolin baya - Gidan Dabino

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!