• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, July 21, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Labarin ‘rasuwa’ ta: Na amsa kiran waya ya fi 500 a yau – Kabiru Nakwango

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
August 8, 2022
in Tattaunawa
1
Alh. Kabiru Abubakar Aliyu (Kabiru Nakwango)

Alh. Kabiru Abubakar Aliyu (Kabiru Nakwango)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

Tun da safiyar ranar Litinin ɗin nan, 8 ga Agusta, 2022 aka tashi da labarin wai tsohon jarumin fim Malam Kabiru Nakwango ya rasu. A cikin ɗan lokaci kaɗan labarin ya bazu a soshiyal midiya kamar wutar daji.

Abin sai ya yi kamar ya lafa sai a ƙara bijiro da shi, don haka labarin ya ci gaba da yaɗuwa tsawon wuni guda. Hakan ya sa jama’a su ka kasa gane tantance gaskiyar maganar.

Ko mu ma a mujallar Fim mun yi ta buga wayar jarumin, wani ya na ɗagawa ya na cewa labarin ba gaskiya ba ne domin shi Nakwango ya na gona ya na aiki, shi ya sa ya kasa gamsar da mu.

Sai dai bayan sallar magariba wakilin mu ya je gidan sa da ke unguwar Gwammaja cikin birnin Kano domin tabbatar da labarin. Mun yi sa’a a daidai lokacin ya dawo daga gona, ko fitowa bai yi daga cikin motar sa ba. 

FIM: An wayi gari da labarin ƙarya cewa wai ka mutu. Ya ka ji da ka samu wannan mugun labarin?

KABIRU NAKWANGO: To, ni Kabiru Abubakar Aliyu, wanda aka fi sani na da Kabiru Nakwango, ni dai abin da zan ce a game da wannan labarin sai dai na ce Allah ya sauwaƙe, domin ina nan lafiya, Allah ya raya ni har zuwa wannan lokaci da mu ke magana da kai, kuma babu abin da ya same ni.

Kuma yanzu da daddaren daga gona na ke, dawowa ta kenan, ko gida ban shiga ba, don haka ina nan da rai na.

FIM: Ko ya aka yi ka samu wannan labarin?

NAKWANGO: To, ni ban karanta labarin ba, kuma ban samu labarin ba, sai dai mutane da su ka karanta su su ka kira ni su ka faɗa mini. Kuma na amsa kiran waya a yau daga safe zuwa yanzu ya fi ɗari biyar. Kuma aboki na Malam Garba shi ya riƙe wayoyin. Duk wayoyi na guda biyu sai da cajin su ya ƙare saboda kira; ɗayar da ta ke hannu na ita ce ta rage mai caji, kuma ba ta taɓa minti ɗaya ba a kira ba. Saboda haka kira ake ta yi ana tambaya ana jajantawa, ina sanar da mutane cewar ba gaskiya ba ne. Hakan sai ya zamana aikin da zan yi a gona kusan kaso biyu daga cikin uku bai samu ba, saboda mutane su na ta kira su na tambaya.

FIM: Wannan ba shi ba ne karo na farko, a baya ma an taɓa yaɗa irin wannan labarin. To ko ya ka ɗauki wannan lamarin?

NAKWANGO: To, ni dai ga shi lafiya ta ƙalau, babu wata rashin lafiya da na yi. To amma dai abin da zan faɗa wa mutane shi ne yin hakan babu alheri. Domin ka ce mutum ya mutu ba shi zai ƙara masa kwana ba, kuma ba shi zai rage masa kwana ba, kuma ba shi da alaƙa da mutuncin sa ko karamcin sa, ko ɗaukakar sa ko durƙushewar sa. Muhimmin abu shi ne kai da ka rubuta kuma ba haka ba ne, ka ɗaukar wa kan ka wani zunubi, domin duk mai son sa idan ya ji sai hankalin sa ya tashi. Don haka kuskure ne. Kuma mutuwa duk in da ka gan ta, abin da za a yi ne aka yi. Saboda haka babu wani abu na mamaki don kare ya yi haushi. Mutuwa abin da za a yi ne aka yi. To an yi, don haka idan ta zo kan Nakwango zai mutu.

FIM: Ko dai don daɗewar da aka yi ba a ganin ka a fim ne ta jawo wannan ji-ta-ji-tar?

NAKWANGO: Ai kafin na fara fim an san ni a wurare daban-daban. Su da su ka daina gani na a wancan wuraren ya su ka yi? Kuma waɗanda su ka daina gani na a fim ya su ka yi? Ba cewa aka yi Nakwango ya daina yin fim ba, kuma ba cewa aka yi Nakwango ba zai yi fim ba, ko wani ne ya hana shi.

Wannan ba wani abu ba ne, a karan kai na ne na ji gara na ke ɗan hutawa domin babu dalilin da zai sa ka yi ta danna abu a kan ka, ka yi ta yi babu ji ba gani. Ina ɗan hutawa; zuwa wani lokaci za ka gan ni jefi-jefi na fito don mutane su gane ina nan da raina kuma ina yin harkar. Ina roƙon Allah ya taimake mu a kan lamuran mu.

FIM: To madalla, mun gode.

NAKWANGO: Ni ma na gode sosai.

Loading

Tags: fake newsGwammajajarumaiKabiru Abubakar AliyuKabiru NakwangoKannywoodKanolabarin ƙaryamutuwarasuwa
Previous Post

Hassada da kutungwilar jami’in gwamnatin Kano ta sa na ja baya da Kannywood – Sani Rainbow

Next Post

Kannywood na buƙatar sabon tsari na zamani – Jammaje

Related Posts

MOPPAN: Za mu haɗa kai da ‘yan siyasa don kawo cigaban Kannywood – Shehu Hassan Kano
Tattaunawa

MOPPAN: Za mu haɗa kai da ‘yan siyasa don kawo cigaban Kannywood – Shehu Hassan Kano

June 30, 2025
Ba faɗuwar zaɓen MOPPAN ta sa muka kafa ƙungiyar NEKAGA ba, inji Ability 
Tattaunawa

Ba faɗuwar zaɓen MOPPAN ta sa muka kafa ƙungiyar NEKAGA ba, inji Ability 

March 1, 2025
Za mu kawo sauyi ga matan Kannywood da tallafin NITDA, inji Mansurah Isah
Tattaunawa

Za mu kawo sauyi ga matan Kannywood da tallafin NITDA, inji Mansurah Isah

November 13, 2024
Bikin auren ‘ya’ya na ya ɗaga daraja ta – Aminu Ala
Tattaunawa

Bikin auren ‘ya’ya na ya ɗaga daraja ta – Aminu Ala

August 2, 2024
Buri na in samar wa MOPPAN tsarin shugabancin da za a riƙa tunawa da ni – Habibu Barde
Tattaunawa

Buri na in samar wa MOPPAN tsarin shugabancin da za a riƙa tunawa da ni – Habibu Barde

March 13, 2024
Mahaifiyar Afakallahu ta kwanta dama
Tattaunawa

Afakallahu: Abin da mahaifiyar mu ta karantar da mu

March 11, 2024
Next Post
Malam Kabiru Musa Jammaje

Kannywood na buƙatar sabon tsari na zamani - Jammaje

Comments 1

  1. Fatee Ahmad says:
    3 years ago

    Allah ya raya mana kae
    Jarumi kabiru na kwango

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!