WASU lauyoyi a Kano sun kai ƙarar mawaƙi Dauda Adamu Abdullahi Kahutu (Rarara) wajen Sarkin Katsina da Sarkin Daura bisa zargin da su ke yi masa na cin zarafin wasu shugabannin siyasa na Jihar Kano a cikin waƙoƙin sa.
Lauyoyin sun roƙi sarakunan da su tsawata masa domin ya tuba kuma ya janye kalaman sa a kan shugabannin tare da neman yafiyar su don a zauna lafiya.
Ɗaya daga cikin lauyoyin, Barista Badamasi Sulaiman Gandu, ya bayyana haka a cikin wata hira da ya yi da gidan rediyon Freedom da ke Kano.
Ya ce tun da farko sun tura wa mawaƙin wasiƙa da ke ɗauke da jan hankali da kira a gare shi da ya tsaftace siyasar shi da salon waƙar sa kasancewar akwai kurakurai da dama a ciki.
Lauyan ya ci-gaba da cewa sun fahimci cewa kalaman da Rarara ke amfani da su a kan shugabannin Jihar Kano sun fara tasiri musamman wajen ƙoƙarin ɓata kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin Katsinawa da Kanawa.
Barista Gandu ya tabbatar da cewa salon waƙoƙin da mawaƙin ke amfani da su sun saɓa wa dokokin ƙasa, domin su kan kawo tarzoma da fitina.
Ya ce haka kuma, bayan cin karo da dokokin ƙasa, waƙoƙin sun saɓa wa koyarwar addinin Musulunci da al’adun mutanen Jihar Kano.
Sannan lauyan ya ƙara da cewa sun rubuta takarda ɗauke da saƙo ga sarakunan da kuma gwamnatin Jihar Katsina da hukumar tsaro don neman a ja masa kunne a matsayin sa na ɗan asalin Jihar Katsina kuma talakan sarakunan.
A wani ɓangaren kuma, Gandu ya nuna takaici bisa waƙar da Rarara ya fitar bayan zaɓen gwamna a Kano wadda ta yi sanadiyyar jawo cin mutunci ga mahaifiyar mawaƙin da wasu ɓatagari su ka yi.
Ya yi fatan matakin da su ka ɗauka zai taimaka wajen dakatar da mawaƙin daga sake yin waƙoƙin cin mutunci ga shugabannin siyasa na Kano kamar yadda su ke zargi.
Wasu daga cikin waɗanda ake zargin mawaƙin ya ci mutuncin su a waƙoƙin sa sun haɗa da tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, tsohon gwamnan Kano kuma tsohon sanata, Rabi’u Musa Kwankwaso, da kuma tsohon gwamnan jihar, Sanata Ibrahim Shekarau.