• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, July 19, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Makarantar Jammaje ta naɗa jarumin Kannywood Abale a matsayin jakaden musamman

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
December 22, 2022
in Labarai
0
Ahmadu Abale (a dama) tare da Malam Kabiru Musa Jammaje

Ahmadu Abale (a dama) tare da Malam Kabiru Musa Jammaje

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MAKARANTAR nan ta koyar da harshen Turanci, Jammaje Academy, ta naɗa jarumin Kannywood, Ahmadu A. Adamu, wanda aka fi sani da Daddy Hikima ko Abale a cikin shirin ‘A Duniya’, matsayin jakaden ta na musamman. 

An yi wa jarumin wannan naɗin ne a wajen taron duniya da makarantar ta shirya a ranar Laraba, 21 ga Disamba, 2022 mai taken ‘Jammaje International Day’ a ɗakin taro na Meena Events Centre da ke Titin Lodge cikin unguwar Nasarawa a birnin Kano.

A cikin jawabin sa, Shugaban makarantar, Malam Kabiru Musa Jammaje, ya bayyana cewa manufar taron ita ce a ƙarfafa wa matasa gwiwa da zaburar da su a kan neman ilimi da sana’o’i don dogaro da kai.

Jammaje, wanda babban furodusa ne a Kannywood, ya ce hakan ne ya sa baya ga koyar da Turanci, makarantar ta samar da wani aji domin koyar da dabarun harkar fim ga matasa, kuma tuni aka fara yaye ɗaliban da aka koyar.

Hagu zuwa dama: Farfesa Mustapha Isa, Mudassir Kasim, Abale, da Kabiru Jammaje lokacin da ake ba Abale satifiket ɗin naɗin sa

Shi ma da ya ke nasa jawabin, babban baƙo a wajen, Farfesa Mustapha Ahmad Isa, ya bayyana cewa irin ƙoƙarin da Jammaje ya ke yi na samar da cigaba ga rayuwar matasa abin a yaba ne.

Dangane da jakadancin da aka bai wa Abale kuwa, cewa ya yi: “Wannan makarantar ta matasa ce da ta ke koyar da matasa karatu da kuma sana’o’i, musamman abin da ya shafi harkar fim, kuma kasancewar Abale matashi kuma ɗan fim da ya ke da ɗimbin jama’a mu ka ga dacewar sa da ya zama jakaden wannan makaranta ta ‘Jammaje Academy’.

Ya ƙara da cewa, “Idan aka duba, shi Malam Kabiru Musa Jammaje matashi ne kuma ya damu da rayuwar matasa, inda ya bayar da lokacin sa wajen koyar da su Turanci, sannan ya zuba kuɗin sa a cikin harkar fim ya yi finafinai da dama, sannan ya zo ya ke koyar da yadda za a yi fim ɗin. Wannan ba ƙaramin aiki ba ne, kuma ya kamata a jinjina masa.

Ya buƙaci matasa da su yi koyi da irin waɗannan ayyukan da Jammaje ya ke yi domin a samar da cigaban rayuwa ga matasan mu na yanzu da kuma masu zuwa nan gaba.

Jammaje (a hagu) tare da Abale

Taron ya samu halartar ‘yan fim da mawaƙan masana’antar Kannywood. Mawaƙa Mudassir Kasim da Salisun Fati da Abdullahi Amdaz sun gabatar da waƙoƙi a wajen.

Loading

Tags: AbaleFarfesa Mustapha Ahmad IsajakadeJammaje AcademyKabiru Musa JammajematasaTuranci
Previous Post

Babu mawaƙiyar da ta yi aure ta daina waƙa a Kannywood – Fa’iza Badawa

Next Post

Karɓuwa ga jama’a: Ba yi na ba ne – Baba Ɗan Audu

Related Posts

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Next Post
Rabi'u Mohammed Rikadawa (Dila ko Baba Ɗan Audu)

Karɓuwa ga jama'a: Ba yi na ba ne - Baba Ɗan Audu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!