• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Makarantar Jammaje ta naɗa jarumin Kannywood Abale a matsayin jakaden musamman

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
December 22, 2022
in Labarai
0
Ahmadu Abale (a dama) tare da Malam Kabiru Musa Jammaje

Ahmadu Abale (a dama) tare da Malam Kabiru Musa Jammaje

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MAKARANTAR nan ta koyar da harshen Turanci, Jammaje Academy, ta naɗa jarumin Kannywood, Ahmadu A. Adamu, wanda aka fi sani da Daddy Hikima ko Abale a cikin shirin ‘A Duniya’, matsayin jakaden ta na musamman. 

An yi wa jarumin wannan naɗin ne a wajen taron duniya da makarantar ta shirya a ranar Laraba, 21 ga Disamba, 2022 mai taken ‘Jammaje International Day’ a ɗakin taro na Meena Events Centre da ke Titin Lodge cikin unguwar Nasarawa a birnin Kano.

A cikin jawabin sa, Shugaban makarantar, Malam Kabiru Musa Jammaje, ya bayyana cewa manufar taron ita ce a ƙarfafa wa matasa gwiwa da zaburar da su a kan neman ilimi da sana’o’i don dogaro da kai.

Jammaje, wanda babban furodusa ne a Kannywood, ya ce hakan ne ya sa baya ga koyar da Turanci, makarantar ta samar da wani aji domin koyar da dabarun harkar fim ga matasa, kuma tuni aka fara yaye ɗaliban da aka koyar.

Hagu zuwa dama: Farfesa Mustapha Isa, Mudassir Kasim, Abale, da Kabiru Jammaje lokacin da ake ba Abale satifiket ɗin naɗin sa

Shi ma da ya ke nasa jawabin, babban baƙo a wajen, Farfesa Mustapha Ahmad Isa, ya bayyana cewa irin ƙoƙarin da Jammaje ya ke yi na samar da cigaba ga rayuwar matasa abin a yaba ne.

Dangane da jakadancin da aka bai wa Abale kuwa, cewa ya yi: “Wannan makarantar ta matasa ce da ta ke koyar da matasa karatu da kuma sana’o’i, musamman abin da ya shafi harkar fim, kuma kasancewar Abale matashi kuma ɗan fim da ya ke da ɗimbin jama’a mu ka ga dacewar sa da ya zama jakaden wannan makaranta ta ‘Jammaje Academy’.

Ya ƙara da cewa, “Idan aka duba, shi Malam Kabiru Musa Jammaje matashi ne kuma ya damu da rayuwar matasa, inda ya bayar da lokacin sa wajen koyar da su Turanci, sannan ya zuba kuɗin sa a cikin harkar fim ya yi finafinai da dama, sannan ya zo ya ke koyar da yadda za a yi fim ɗin. Wannan ba ƙaramin aiki ba ne, kuma ya kamata a jinjina masa.

Ya buƙaci matasa da su yi koyi da irin waɗannan ayyukan da Jammaje ya ke yi domin a samar da cigaban rayuwa ga matasan mu na yanzu da kuma masu zuwa nan gaba.

Jammaje (a hagu) tare da Abale

Taron ya samu halartar ‘yan fim da mawaƙan masana’antar Kannywood. Mawaƙa Mudassir Kasim da Salisun Fati da Abdullahi Amdaz sun gabatar da waƙoƙi a wajen.

Loading

Tags: AbaleFarfesa Mustapha Ahmad IsajakadeJammaje AcademyKabiru Musa JammajematasaTuranci
Previous Post

Babu mawaƙiyar da ta yi aure ta daina waƙa a Kannywood – Fa’iza Badawa

Next Post

Karɓuwa ga jama’a: Ba yi na ba ne – Baba Ɗan Audu

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Rabi'u Mohammed Rikadawa (Dila ko Baba Ɗan Audu)

Karɓuwa ga jama'a: Ba yi na ba ne - Baba Ɗan Audu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!