A DAREN Talata, 28 ga Nuwamba, 2023 Allah ya yi wa Malama Hauwa’u Abubakar rasuwa.
Marigayiyar, mai kimanin shekaru 78 a duniya, ta rasu ne sakamakon wani gajeren rashin lafiya. Ta bar ‘ya’ya biyar – maza biyu, mata uku. Daga cikin su akwai marubuci kuma jami’in yaɗa labarai na Ƙungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA), reshen Jihar Kano, Malam Ibrahim M. Indabawa.
Ana ci gaba da zaman makokin marigayiyar a gidan Ibrahim M. Indabawa da ke unguwar Sharaɗa cikin garin Kano.
Da fatan Allah ya jiƙan ta, ya bai wa iyalai da ‘yan’uwa haƙurin jure wannan babban rashin da aka yi.
![]()







