A RANAR Asabar, 19 ga Agusta, 2023 aka yi wani ɗan ƙwarya-ƙwaryan taro don tattaunawa a kan makomar rubutun zube na Hausa.
‘Ya’yan Kano Book Club ne su ka shirya taron a Kano, wanda Malam Abubakar Muhammad da ke koyar da harshen Hausa a Amurka ya shirya.
Taron, wanda ya gudana bisa jagorancin Malam Ismail Bala, tsohon shugaban ƙungiyar marubuta ta kasa ANA reshen Jihar Kano.
Ya samu mahalartar ɓangarori da dama na marubuta da masu ruwa da tsaki a harkar rubutu. Sun haɗa da Dr. Ibrahim A. Bichi, tsohon shugaban ɗakunan karatu na Jihar Kano, da tsofaffin marubuta da na zamani, musamman waɗanda ake kira ‘online writers’.
Waɗannan marubuta sun ƙunshi Bala Anas Babinlata, Umma Sulaiman ‘Yan Awaki Sadiya Garba Yakasai, Muhammad Lawal Barista, Kabiru Yusuf Anka, Ibrahim M. Indabawa, Kamilu D. Gwammaja, da sauran su.

A jawabin sa, Malam Abubakar Muhammad ya bayyana dalilin sa shirya taron. Ya ce ya yi tunanin shirya taron ne saboda matsalar littattafan zube na Hausa masu inganci da su ke fuskanta a ƙasashen Turai, a yayin koyar da harshe da al’adu. Hakan ya shafi fassara daga Hausa zuwa Turanci, wanda babu wadatattun littattafai kuma masu inganci.
Manufar taron dai shi ne a tattauna tare da tunanin yadda za a yi maganin matsalolin.
Kafin a fara taron dai sai da aka saurari wani faifan bidiyo daga Dakta Umma Aliyu da ke koyar da harshen Hausa a ƙasar Jamus. Ita ma ta yi jawabi ne a kan wannan matsala ta rashin littattafai masu inganci da abin da ya kamata a yi.
A ƙarshen taron, an yi nasarar tattauna abubuwa da dama, inda aka yanke za a sake shirya wani zaman don tunanin fitar da mafita a kan matsalolin da aka fitar.


Yau kuma Ni ne na zama malam Abubakar Muhammad? Ikon Allah.