AN bayyana cewa tauye haƙƙin mata da marubuta maza su ke yi wani abu ne da ya daɗe kuma har yanzu sai ƙara ci gaba ya ke yi.
Marubuciya kuma malamar makaranta, Dakta Maryam Ali Ali, ita ce ta bayyana haka a lokacin da ta ke tsokaci a wajen taron da marubuta su ka shirya a ranar Lahadi da ta gabata a Kano.
Dakta Maryam, wadda babbar malama ce a Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kano, ta faɗa wa mahalartan taron cewa: “Su maza ba za su rabu da son kan su ba a duk wata harka ta rayuwa, don haka ko a wannan taron ma sai da su ka nuna halin nasu na son kai. Don haka tun da aka fara taron har zuwa yanzu babu wata marubuciya mace da aka ambata a matsayin gwarzuwar da ta bayar da gudunmawa a cikin adabin Hausa; duk wanda ya zo jawabin sa sai ya ambaci maza marubuta a matsayin waɗanda su ka bayar da gudunmawa, duk da kowa ya san mace ce farkon marubuciya a adabin Hausa, wato Hafsat Abdulwahid, amma har aka kusan tashi daga taron nan ba a ambaci gudunmawar da ta bayar ba.”
Malamar, wadda ita ce ta rubuta littafin ƙirƙira mai suna ‘Fuskokin Naira’, ta ƙara da cewa, “Bayan ita, akwai manyan marubuta mata irin su Bilkisu Salisu Funtua, Balaraba Ramat, da sauran su, amma su da yake mata ne kamar babu wata gudunmawa da su ka bayar.
“Wannan kuma ɗabi’ar maza ce ba tun yanzu ba. Domin ko a lokacin Manzon Allah (s.a.w.) da aka zo rubuta sunayen gwaraza saboda son kai na maza sai su ka rubuta littafi ‘Arrijalu Haula Rasulu’. Sai daga baya da aka yi magana, su ka dawo su ka rubuta ‘Annisa’u Haula Rasulu’.
“Don haka wannan wani abu ne sananne a tarihi na tauye haƙƙin mata da maza su ke. Mu kuma ba za mu zuba ido mu na kallon ana tauye mana haƙƙi ba, don haka in dai za a yi taro a faɗi gwarazan marubuta, to tarihin rubutun Hausa ba zai cika ba sai an haɗa da mata. Saboda haka ya zama dole a gyara in dai ana son a yi adalci.”