
MUHAMMAD, ɗan jarumi kuma Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Dab’i ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya cika shekaru 10 cif a duniya.
Muhammad Abba El-Mustapha shi ne na biyu a cikin ‘ya’ya ‘ya’ya uku da jarumin yake da su. Ya na ‘yan’uwa mata guda biyu.
A ranar Asabar, 29 ga Yuni, 2024 El-Mustapha ya shirya wa Muhammad bikin taya shi murna da kuma nuna godiya ga Allah bisa cikar sa shekaru 10.
Ba wani taro na mutane da yawa aka yi ba, an dai shirya taro ne na gida wanda iyaye da ‘yan’uwan Muhammad ɗin da abokan sa na kusa su ka halarta.

An yi ƙwarya-ƙwaryar liyafar cin abinci tare da yanka kek. Daga nan aka yi addu’a.
El-Mustapha ya nuna farin ciki tare da godiya ga Allah, ya na mai fatan Allah ya raya Muhammad cikin aminci da sauran ‘yan’uwan sa da dukkan al’ummar Musulmi.



![]()






