• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ranar 1 ga Disamba za a fara taro kan nuna finafinai da waƙoƙin Nijeriya ta hanyar intanet

by DAGA IRO MAMMAN
November 28, 2021
in Labarai
0
Wasu fitattun kamfanonin watsa shirye-shirye ta hanyar intanet (wato 'OTT'). Hoto daga: ColowWhistle

Wasu fitattun kamfanonin watsa shirye-shirye ta hanyar intanet (wato 'OTT'). Hoto daga: ColowWhistle

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Tace Finafinai ta Ƙasa (NFVCB) ta ce taron nan wanda ta ce za ta yi da kamfanonin watsa finafinai a intanet da tashoshin talbijin na satalayit, yanzu za a yi shi ne a ranakun Laraba da Alhamis mai zuwa, wato 1 da 2 ga Disamba, 2021.

A cewar ta, taron ya zama wajibi ne saboda ƙasashen duniya su na damuwa kan irin abubuwan da ake ƙirƙira ana yaɗawa a cikin bidiyo da finafinai ta hanyar intanet da tashoshin talbijin na satalayit da yadda su ke shafar al’adu ko kawo illa a cikin al’umma, da kuma matsayin gwamnatoci wajen kawo gyara a cikin su.

Idan kun tuna, a ranar 11 ga Nuwamba, 2021 mujallar Fim ta ba ku labarin cewa hukumar za ta yi wani gagarumin taro don tattaunawa da masu ruwa da tsaki da kuma kamfanonin da ke yaɗa irin waɗannan finafinai da bidiyo, waɗanda ake kira kamfanonin yaɗa ‘OTT’.

‘OTT’ (wato ‘over-the-top’) su ne finafinai, waƙoƙi ko shirye-shiryen talbijin da wasu kamfanoni ke tura wa mai buƙata ta hanyar intanet a bisa irin buƙatar sa, kuma zai riƙa biyan kuɗi, wato irin su Netflix, Amazon, Showmax, Africa Magic, YouTube, Iroko TV da ire-iren su da ke Nijeriya.

Labarin ya biyo bayan wani taro da Alhaji Adedayo Thomas ya yi da manema labarai a Legas.

Alhaji Adedayo Thomas, Babban Daraktan NFVCB

Taken taron da za a yi a wannan makon shi ne, “Al’amuran Dokokin Tace Finafinai na Nijeriya da Tsarin Kawo Gyara Ga Kamfanonin Yaɗa Finafinai da Bidiyo da Masu Ƙirƙirar Shirye-shiryen Kallo,” wato a Turance, “Implications of Nigerian Censorship Laws and Regulatory Framework for OTT Streaming Services and Content Providers”.

A sanarwar da daraktan hukumar mai kula da shiyyar arewa-maso-yamma, Malam Umar G. Fage, ya ba mujallar Fim, an bayyana cewa, “Wannan muhimmin taro zai kuma yi nazari kan babban lamarin nan na samar da kyakkyawan yanayi ga kamfanonin yaɗa shirye-shirye don su haɓaka aikin su.”

Za a yi taron ne a otal ɗin Marriot da ke unguwar GRA, Ikeja, a Legas a ranar Laraba mai zuwa, 1 ga Disamba da kuma washegarin ranardaga ƙarfe 9:00 na safe a kullum.

Sanarwar ta ce babban mai masaukin baƙi a taron shi ne Ministan Yaɗa Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed, yayin da Shugaban Hukumar Tace Finafinai ta Ƙasa, Alhaji Adedayo Thomas, zai kasance mai masaukin baƙi.

Loading

Tags: adedayo thomascensorshiphausa filmsKannywoodNational Film and Videos Censors BoardNetflixNFVCBOTTOver the Top contentUmar G. FageYouTube
Previous Post

Hamisu Jibrin Goma ya zama sabon shugaban masu shirya fim na Kaduna

Next Post

Jaruma Maryam Waziri da ɗan ƙwallo Tijjani Babangida sun angwance

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Amarya Maryam Musa Waziri da angon ta Tijjani Babangida su na yi wa juna kallon ƙuda

Jaruma Maryam Waziri da ɗan ƙwallo Tijjani Babangida sun angwance

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!