AN kwantar da Babban Sakataren Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), Malam Salisu Mu’azu, a asibiti bayan wani hatsarin mashin da ya ritsa da shi a daren ranar Asabar.
Fitaccen mawaƙi Misbahu M. Ahmad, wanda ya fitar da sanarwar rashin lafiyar a cikin wani saƙon murya da ya yaɗa a soshiyal midiya, ya ce haɗarin ya auku ne bayan da wani direban Adaidaita Sahu ya buge Salisun a kan Titin Maiduguri da ke Ƙaramar Hukumar Tarauni a Jihar Kano.
Ya ce har ta kai ga Salisun ya samu karayar ƙashi a kwankwason sa.
An garzaya da shi asibitin ƙashi na Al-Amin da ke Titin Maiduguri.
Misbahu ya, ce, “Iftila’in ya faru ne a daren ranar Asabar, inda wani ɗan Adaidaita Sahu ya buge shi kuma ya yi masa illa sosai domin ya karya masa wani ƙashi da ke saman cinyar sa, wato kwankwaso.”
Ya ƙara da cewa, “Cikin yardar Allah yanzu an samu an kai shi asibiti a safiyar ranar Lahadi, tare da yi masa aiki a gun da ya samu karayar.”
Misbahu M. Ahmad ya ƙarƙare da neman addu’ar al’umma domin Allah ya ba Salisu Mu’azu lafiya.
Subhanallah Allah ya bashi lafiya , Allah sa zakka ne aminn
Allah yabashi lpy