FITACCEN jarumi kuma mawaƙi Umar M. Shariff ya bayyana cewa ba zai taɓa mantawa da nasihar da mahaifin sa ya riƙa yi masa ba kafin rasuwar sa a jiya.
Ya faɗi haka ne a lokacin da ya ke zantawa da mujallar Fim a yau a wajen zaman makokin rasuwar mahaifin nasa da ake yi a gidan su da ke Layin ‘Yankifi, unguwar Rigasa, cikin garin Kaduna.
Shi mahaifin na su Umar, wato Malam Muhammad Shariff, ya rasu ne a daren jiya Litinin, 2 ga Maris, 2020 a Asibitin Sultan da ke Titin Maƙarfi, a Rigasa, Kaduna.
Marigayin, mai kimanin shekara 75 a duniya, ya rasu ne bayan ya sha fama da rashin lafiya.
An yi masa sallah da misalin ƙarfe 8:30 na safe a gidan sa.
Mamacin ya rasu ya bar mata ɗaya da ‘ya’ya takwas – maza 3, mata 5.
A cikin ‘ya’yan akwai fitattun ‘yan fim su uku, wato Umar M. Shariff, Abdul M. Shariff da Mustapha M. Shariff.
Umar dai mawaƙi ne jarumi. Haka shi ma yayan sa Abdul jarumi ne yayin da babban yayan su, Mustapha, shi kuma darakta ne, kuma mai koyar da rawa a Kannywood.
‘Yan fim da mawaƙa da dama sun halarci jana’izar dattajon, kuma sun je gaisuwa.
Sun haɗa da Abdullahi Abbas, Malam Yahaya Makaho, Abu Sarki, Sulaiman Sir Zeesu, Abdul D. One, Sadiqu Atis, Sabi’u Gidaje, Haruna Gidaje, Nafi’u Gidaje, Ubale 2-Effects, Ɗanladiyo Mai Atamfa, Ibrahim Shasha, Alfazazi Muhammad, Mai Gala, Yusuf Lazio, Abdul FKD, Tukur Musa TK, Abdullahi Jiya Da Yau, Ibrahim Usman (Liti), da sauran su.
A wajen zaman makokin ne mujallar Fim ta yi wa Umar M. Shariff ta’aziyya tare da tambayar sa abin da zai ce game da wannan babban rashi.
Sai ya amsa da cewa: “Da farko dai ina yi wa Allah godiya, wanda shi ne ya tsara wannan al’amari, kuma babu wanda zai iya canzawa.
“Kuma mu na farin ciki da hakan, musamman ganin ta hanyar rashin lafiya ne, kuma mun yi iya ƙoƙarin mu don ganin cewa mun ceto rayuwar sa, amma tun da Allah ya nufa, haka ya tsara masa rayuwar sa, to mu na farin ciki da dukkan hukuncin da Allah ya ɗauka a kan sa.
“Don haka mu na yi masa addu’ar Allah ya yi masa rahama, ya kuma gafarta masa.”

Da wakilin mu ya tambaye shi abin da mahaifin nasu ya ke yawan faɗa masa wanda ba zai taɓa mantawa da shi ba, sai Umar ya ce, “Gaskiya, abubuwan da yawa. Saboda kullum idan za mu zauna da shi nasiha ce kawai tsakanin mu, nasiha ta yadda za mu zauna da kowa lafiya, yadda za mu gudanar da al’amuran rayuwa da kuma yadda za mu bi sauran abubuwa yadda su ka da ce.
“Kullum nasihar sa kenan a gare mu.
“Hatta lokacin da ya ke kwance a kan gadon asibiti, sai da ya yi mana wannan nasiha ta mu zauna da kowa lafiya, mu ji tsoron Allah, kuma duk abin da za mu yi mu nemi halal ɗin mu.
“Wannan shi ne abin da ba zan taɓa mantawa ba in na tuna da mahaifin mu.”
To, Allah ya jiƙan Malam Muhammad, ya sa mutuwar sa hutu ce, amin.

