• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Yadda Gwamnan Kano ya naɗa ni mai taimaka masa kan harkar jinƙai da agaji – marubuciya Fauziyya D. Sulaiman

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
August 24, 2023
in Labarai
0
Hajiya Fauziyya D. Sulaiman

Hajiya Fauziyya D. Sulaiman

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNAN Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya naɗa fitacciyar marubuciya Fauziyya D.  Sulaiman muƙamin babbar mai taimaka masa kan harkokin jinƙai da agaji ga mabuƙata.

Fauziyya ita ce shugabar wata gidauniya mai zaman kan ta a Kano mai suna ‘Creative Helping Needy Foundation‘ kuma ta yi fice wajen nema wa mabuƙata, musamman marasa lafiya, taimako a wajen jama’ar Annabi.

Marubuciyar littattafai ce wadda kuma ke rubuta labarin fim (screenplay). Haka kuma ma’aikaciya ce a gidan talbijin na Arewa 24 da ke Kano.

An yi sabon naɗin ne a yau, kamar yadda marubuciyar da kan ta ta sanar a wani saƙo da ta wallafa a soshiyal midiya.

A rubutun da ta yi kan yadda ta samu labarin naɗin nata, Fauziyya ta labarta wa duniya cewa: “Ɗazu wani ya kira ni ya gaya mun suna meeting  da mai girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi ta ambaton irin aikin da nake yi saboda yana bibiyar shafi na, ya ce, ‘Tabbas kina abu mai kyau, ki ci gaba.’ Na yi godiya.

Takardar naɗa Fauziyya D. Sulaiman da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rubuta da hannun sa

“Da la’asar kuma sai abokin aiki na, Nasir Nid, ya shigo ofis  yana dariya, ya ce, “Uwar marayu, mai girma Gwamna ya ba ki muƙami a kan aikin ki na jinƙai.’ Na ce, ‘Tsokana ta kake.’

Ya yi ta rantsuwa, muna dariya.

“Zuwa can sai ga kiran Sunusi Oscar, ya ce mini, ‘Hajiya Fauziyya, mai girma Gwamna ya ba ki muƙamin SSA.’ Na ce, ‘Ni kuma?’ Ya ce, ‘E, yanzu haka muna meeting da shi, zan kira ki idan mun kammala.’

“Zuwa can ya kira ya ce mu haɗu. Bayan mun haɗu ya ba ni takardar nan, ya ce, ‘Mai girma Gwamna ne ya ce a ba ki.’

“Na riƙe baki da mamaki, na ce, ‘Ni da ba ‘yar siyasa ba yaya za a ba ni muƙami?’

“Sai ya ce, ‘E, ai da man ba a kan siyasa aka zaɓe ki ba. Mai girma Gwamna ya ba ki muƙami a kan aikin da kike yi na tallafi da jinƙai domin yana ganin aikin ki yana bin fejin ki hankalin sa yana tashi a kan duk abin da kike sakawa. Ga takardar ki. Amsa.’

“Na amshi takardar na kalla, na ce, ‘Yanzu wannan daga  hannun gwamna take?’

“Ya ce, ‘Ƙwarai kuwa. Duk Kano wa ya isa ya yi rubutu da jan biro idan ba gwamna ba?’

Fauziyya na karɓar naɗin ta daga hannun Mataimaki na Musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Alhaji (Oscar 442), a ofishin sa

“Kamar dai yadda kuke ganin wannan takarda, mai girma Gwamnan Kano  ya ba ni muƙamin SENIOR SPECIAL ASSISTANT, NEEDY AND VULNERABLE. Ina godiya ƙwarai da gaske ga mai girma Gwamna.

“Ina neman addu’ar ku bisa wannan nauyi da mai girma Gwamna ya ɗora mini, ‘yan’uwa.

“Allah ya sa ya zama alkairi ga al’ummar Jihar Kano. Allah ya ba ni ikon cinye jarrabawar da ke tattare da wannan nauyin, amin ya Allah.”

Wani hoton inda Fauziyya ke karɓar naɗin ta daga hannun Sunusi Oscar 442

Labarin wannan naɗi ya yi wa masoyan Fauziyya daɗi, musamman ma marubuta. Tuni dai ‘yan’uwa da abokan arziki suka shiga aikawa da saƙon taya ta murna tare da yi matan fatan Allah ya taya ta jagoranci.

Loading

Previous Post

Masana da marubuta sun yi taro kan ingancin rubutu a Kano

Next Post

Waƙoƙin mu ba na batsa ba ne, na faɗakarwa ne – Hadiza Maikano

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Hajiya Hadiza Maikano

Waƙoƙin mu ba na batsa ba ne, na faɗakarwa ne - Hadiza Maikano

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!