A DAREN Litinin, 9 ga Oktoba, 2023 Allah ya azurta jarumin Kannywood, Yusuf Muhammad Abdullahi (Sasen), da santalelen ɗa namiji.
Maiɗakin sa, Ameena Zakari Yunusa, ta haihu ne a wani asibitin kuɗi mai suna MGK, daura da Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano a birnin Kano.
Yusuf Sasen, wanda aka fi sani da Lukman a cikin shirin ‘Labari Na’, ya yi wa jaririn nasa huɗuba tare da raɗa masa suna Muhammad Auwal.
Idan ba ku manta ba, an ɗaura auren Yusuf da Ameena a ranar Asabar, 24 ga Disamba, 2022 a garin Potiskum, Jihar Yobe.
Allah ya raya Muhammad Auwal bisa turbar addinin Musulunci, amin.