• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, July 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Kannywood sun ƙi ni saboda ni Kirista ne, Nollywood kuma saboda ni ɗan Arewa ne – Darakta Prince Daniel Aboki

by ALI KANO
March 22, 2025
in Labarai
0
Kannywood sun ƙi ni saboda ni Kirista ne, Nollywood kuma saboda ni ɗan Arewa ne – Darakta Prince Daniel Aboki

Prince Daniel

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

DARAKTAN fim ɗin ‘Mai Martaba’, wato Prince Daniel Aboki, ya bayyana cewa lokacin da ya so shiga harkar fim a Arewa sai ‘yan Kannywood suka ƙi karɓar sa, da ya koma kudu kuma sai su ma ‘yan Nollywood suka ƙi karɓar sa yadda ya kamata.

Jaridar online ta Pulse Nigeria ta ruwaito shi yana cewa dalilin ƙin sa a Arewa, saboda shi Kirista ne, ita kuma Kannywood ta Musulmi ce, yayin da ita kuma Nollywood yawanci ta Kiristocin Kudu ce, ga shi kuma shi ɗan Arewa ne.

Ta ce Daniel Aboki ya yi wannan tsokacin ne a wurin bikin baje-kolin finafinai na shekara-shekara na 2025 da ake kira Nollywood in Hollywood, a birnin Los Anjalis, Jihar Kalifoniya, a ƙasar Amurka.

An yi bikin a gidan wasa na Egyptian Theatre a cikin masana’antar Hollywood da kuma Jami’ar Southern California (USC) daga ranar 28 ga Fabrairu zuwa 1 ga Maris, 2025.

Mashiryin fim ɗin, ma’aikacin rediyo ne wanda a yanzu yake tashe a harkar shirya finafinai ta Nijeriya, musamman daga lokacin da aka shigar da fim ɗin sa na ‘Mai Martaba’ a matsayin wakilin Nijeriya a gasar duniya ta Oscars.

A cewar sa, ya fuskanci tsana daga Kannywood da Nollywood ne saboda inda ya fito.

Da yake amsa tambayoyin mahalartan taron, daraktan wanda ya ci kyaututtukan karramawa da dama a wurare daban-daban, ya faɗi irin gwagwarmayar da ya sha, ya ce: “Na samu kai na a tsaka-mai-wuya saboda ni ɗan Arewa ne, amma kuma Kirista.

“Ita Kannywood, da yake yawancin ta industirin Musulmi ce, ba ta karɓe ni sosai ba. A ɗaya ɓangaren kuma, su ma Nollywood, wadda yawanci Kiristoci ne, ba su karɓe ni ba saboda ni ɗan Arewa ne. Sai na samu kai na ina lilo a tsakanin duniyoyi biyu.”

Daga hagu: Abraham Awam-Amkpa, jarumin ‘The Man Died,’ da Uzoamaka Aniunoh, jarumar ‘The Weekend’, da Prince Daniel Aboki, daraktan ‘Mai Martaba’ a bikin baje-kolin finafinai na Nollywood in Hollywood wanda aka yi a birnin Los Anjalis. Hoto na dama kuma Prince Daniel ne a taron

A cewar sa, ya samu sauyin rayuwa ne daga lokacin da aka zaɓi ‘Mai Martaba’ a matsayin fim ɗin da zai wakilci Nijeriya a gasar Oscars.

Ya ce: “Abubuwan sun canja ne daga lokacin.”

Bayan wannan ƙi da aka nuna masa, Prince Daniel Aboki ya kuma haɗu da wahalhalun rashin kuɗi. “Ba wanda yake so ya zuba jari domin dai ni ba sanannen darakta ba ne,” inji shi.

Wata matsalar kuma ita ce samun lokeshin inda babu tashin hankali saboda matsalar tsaro da ake fama da ita a Arewa.

Ya ce: “Saboda barazanar Boko Haram da sace mutane da ake fuskanta, sai da muka bi a hankali wajen zaɓen wurare masu kwanciyar hankali.

“A ƙarshe dai mun ɗauki fim ɗin a Daura, wato garin su tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.”

Babbar matsalar da su Prince Daniel Aboki suka fuskanta ita ce da suka yi asarar sama da rabin fim ɗin da suka ɗauka saboda shirmen da wani ya yi masu.

Ya ce: “Mun yi asarar kimanin kashi 46 cikin ɗari na dukkan aikin da muka yi.” Da faɗin haka, sai masu sauraren sa a taron suka ja numfashi saboda mamaki.

Ya ce maganin matsalar kaɗai shi ne tilas suka sake ɗaukar aikin.

A ƙoƙarin sa na ceto fim ɗin, Aboki ya nemi shawarar mai kular masa da editin fim ɗin don jin yadda za su yi. Ta ce: “Na kira shi na tambaye shi idan akwai abin da za a iya yi. Sai ya ba ni amsa da wata aya daga cikin Baibul da ta ce: ‘Za a tashi ƙasusuwan da suka bushe’.”

Ya ce: “Abin da kuke gani yanzu shi ne wani sabon ɗaukar fim ɗin. Ba ma alfahari da abin da ya faru, to amma gaskiyar lamarin kenan.”

Loading

Tags: KannywoodnollywoodPrince Daniel
Previous Post

Gwamnatin Tarayya ta jaddada ƙudirin kare ‘yancin faɗin albarkacin baki da ‘yancin ‘yan jarida

Next Post

Kannywood ba ta taɓa ƙyama ta saboda addini na ko ƙabila ta ba — Prince Daniel

Related Posts

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Next Post
Kannywood ba ta taɓa ƙyama ta saboda addini na ko ƙabila ta ba — Prince Daniel

Kannywood ba ta taɓa ƙyama ta saboda addini na ko ƙabila ta ba — Prince Daniel

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!