NAFISA Mas’ud, ɗiyar tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Sulaiman, ta kammala haddar Alƙur’ani mai tsarki tare da shiga cikin ɗaliban da aka yaye a makarantar Islamiyyar su.
An gudanar da bikin saukar Alƙur’ani na Nafisa, mai shekaru 17 a duniya, a ranar Lahadi, 28 ga Yuni, 2026, a harabar makarantar Islamiyyar su da ke unguwar Rijiyar Zaki a birnin Kano.
Bikin ya samu halartar mahaifiyar ta, Fati Sulaiman, tare da ‘yan’uwa, abokan arziki da sauran masu fatan alheri, waɗanda suka taru domin taya ta murnar wannan babban rabo na kammala haddar littafin Allah.

Nafisa ta kasance cikin ɗaliban da makarantar ta yaye bayan sun kammala haddar, lamarin da ya jawo farin ciki da godiya ga iyalan ta da sauran masu ƙaunar ta.
Mahalartan taron sun yi addu’ar Allah ya ƙara mata ilimi mai amfani, ya tabbatar da ita a kan koyarwar Alƙur’ani, tare da sanya wannan nasara ta zama alheri gare ta a duniya da lahira.



![]()







