• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Abin da ya sa mu sha’irai ba mu da haɗin kai – Bashir Ɗanɗago

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
September 29, 2022
in Mawaƙa
0
Malam Bashir Ɗandago

Malam Bashir Ɗandago

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MAWAƘIN yabon Annabi (s.a.w.), Malam Bashir Ɗandago, ya bayyana cewa rashin haɗin kan da ke tsakanin sha’irai shi ne ummulhaba’isin koma-bayan da harkar tasu ta ke ciki.

Malam Bashir, wanda da shi aka fara harkar bege kusan shekara arba’in da ta gabata, ya bayyana hakan ne a lokacin tattaunawar sa da mujallar Fim kan matsalolin da ke faruwa a cikin harkar sha’irai, musamman ma a yanzu da jama’a su ka yi yawa a cikin ta.

A cewar sa: “Tun a farko aka samar da wannan matsalar, tun a lokacin da mu ka sharafin mu, to a lokacin sai ya zama mun samu masu kula da mu tsakanin su da Allah, sai ya zama a cikin mu mu ka samar da matsalar, don mun samu masu kuɗi da su ka riƙa yi wa mawaƙan Annabi hidima iya ƙoƙarin su har da ba da kujerar Makka. 

“To amma sai ya zama mu a kan mu da ya kamata a ce mun riƙe abin da hannu biyu, kuma ba mu yi ba. Don su masu yi wa Annabi hidimar, an shiga inuwar su an yi masu dashi, duk sai su ka ja baya da kulawar da su ke yi mana.

“Don haka daga an ji wani mai ki da ya ke son yin hidimar Annabi, sai wasu su je a guje su kewaye shi su hana kowa ya je wajen. Kuma idan su ka tarar da wani a wajen, to sai sun yi yadda su ka kore shi. 

“Don haka harkar yabon Annabi a yanzu sai dai mu ce inna lillahi, don ba a ganin girman masu girma.

“Wannan ya sa samar da ƙungiyar da za ta wakilce mu a gwamnati ta gagara.

“Akwai lokacin da aka kira mu, mu sha’irai, mu ka tattauna da gwamna, inda mu ka faɗa masa buƙatun mu: mu na so a samar da mai ba gwamna shawara a kan sha’irai. Kuma an amince da hakan, aka ce mu samar da wani daga cikin mu.

“Tun da mu ka taso abin bai yiwu ba saboda mun kasa fitar da wanda zai riƙe muƙamin a cikin mu, saboda kowa bai yarda da kowa ba. 

“Da na kira Yusuf Tumfafi, mai ba gwamna shawara a kan harkar ƙungiyoyi, na tambaye shi halin da ake ciki, sai ya ce, ‘Ai kun kasa haɗa kan ku, don wasu daga cikin ku su na ta bugo waya su na cewa su fa idan wane ne to ba za su amince ba. Don haka abin ya yi yawa, mu ka rabu da ku.’

“Irin wannan halin harkar yabon Annabi ta ke ciki; duk an bi an saka son zuciya da son girma.”

Da wakilin mu ya tambaye shi yadda za a yi a gyara matsalar a matsayin sa na uba a cikin harkar, sai Malam Bashir ya ce, “A gaskiya tun da Hukumar Tace Finafinai ta kasa haɗa kan sha’irai, ai ina ganin a jira a gani kawai daga Allah. Saboda hukumar ta shiga ta yi wa kowa rajista, to amma matsalar a jagorancin ta ke; duk wanda aka ɗauko aka ɗora shi, sai ya saka son rai a ciki. Shi kuma shugaban Hukumar Tace Finafinai ya ɗauki abin da zafi, sai ya zama ƙarshe abin ya yi shiru.

“Don haka tun da Hukumar Tace Finafinai ta gaza, to fa abin sai dai addu’a.”

Mawaƙin ya yi kira ga sha’irai da cewa su sani harkar yabon Annabi su ke yi, don haka ya kamata a riƙa ganin siffar Annabi a wajen aikin su da kuma mu’amalar su da jama’a.

Loading

Tags: Annabi (s.a.w.)Bashir ƊandagoBegegwamnahaɗin kaiHukumar Tace FinafinaimawaƙawakilciYusuf Tumfafi
Previous Post

Buƙatar na sauya akalar siyasar da ake yi ya sa na tsaya takara – Aminu Ala

Next Post

Furodusa Maishadda ya bayyana sirrin nasarar da ya samu a Kannywood cikin shekara 10

Related Posts

Za a gabatar da littafin waƙoƙin Salma ɗiyar marubuciya Halima K Mashi ran Asabar
Mawaƙa

Za a gabatar da littafin waƙoƙin Salma ɗiyar marubuciya Halima K Mashi ran Asabar

August 23, 2026
‘Ya’ya biyu mata na Mudassir Kasim sun yi saukar karatun Alƙur’ani
Mawaƙa

‘Ya’ya biyu mata na Mudassir Kasim sun yi saukar karatun Alƙur’ani

August 2, 2026
Sani Danja: Waƙar ‘Barau Jigijim’ ta tayar da ƙura, ya ƙaddamar da gasa a kan ta
Mawaƙa

Sani Danja: Waƙar ‘Barau Jigijim’ ta tayar da ƙura, ya ƙaddamar da gasa a kan ta

July 15, 2026
Za a yi bikin naɗa Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa a Daura ranar Asabar
Mawaƙa

Za a yi bikin naɗa Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa a Daura ranar Asabar

December 11, 2025
Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi
Mawaƙa

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

April 19, 2025
Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala

October 28, 2024
Next Post
Abubakar Bashir Maishadda

Furodusa Maishadda ya bayyana sirrin nasarar da ya samu a Kannywood cikin shekara 10

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!