ALLAHU Akbar! Da safiyar wannan rana ta Laraba, 23 ga Nuwamba, 2022 ne Allah ya karbi ran ɗan wasan barkwanci Malam Sa’idu Ado Gano (wanda aka fi sani da suna Bawo) rasuwa.
Majiya ƙwaƙƙwara ta shaida wa mujallar Fim cewa ya rasu ne a gidan sa da ke garin Gano a Ƙaramar Hukumar Dawakin Kudu a Jihar Kano bayan rashin lafiya da ya yi fama da shi.
Marigayin dai ya na ɗaya daga cikin ‘yan wasan barkwanci da su ka rage a cikin abokan tafiyar marigayi Rabilu Musa Ɗanlasan (Ibro).
Tuni aka yi jana’izar sa kamar yadda addinin Muslumci ya tanadar.
Allah ya jiƙan sa da rahama, amin.
![]()







