• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 1, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Bidiyon baɗala: Hukuma ta wanke jarumar Kannywood Maryam Yahaya

by DAGA ABBA MUHAMMAD
January 4, 2024
in Labarai
0
Bidiyon baɗala: Hukuma ta wanke jarumar Kannywood Maryam Yahaya

Maryam Yahaya: Ba ita ba ce a ciki

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano ta bayyana cewa ba ta kama jarumar Kannywood Maryam Yahaya da wani laifi ba game da wani faifan bidiyo da aka yaɗa a soshiyal midiya na wani saurayi da wata budurwa da ta ke yi wa saurayin goge.

Sai dai wannan bidiyo na nuna cewa kamar a wurin bikin auren su ne su ka yi, domin ita budurwar shigar amare ta yi.

An ɗauki bidiyon tare da manna hotunan Maryam Yahaya a cikin bidiyo a nana cewa jarumar ce ta ke yi wa wani saurayi gogen.

An haɗa hotunan Maryam da na wasu matasa don a yaudari mutane

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Malam Abdullahi Sani Sulaiman, ya ce, “Biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da mu ka karɓa a kan wani bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta na zamani, wanda ke nuna wata matashiya da ake zargin jarumar finafinan Hausa ce ta Kannywood, wato Maryam Yahaya, da yin bidiyon da ya ci karo da dokokin Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano.

“A saboda haka, mun gudanar da bincike na musamman tare da samun rashin sahihanci na wannan bidiyo da aka tura mana ƙorafi a kai.”

Ya ci gaba da cewa, “Haka kuma, binciken ya tabbatar da fuskar wacce ta yi bidiyon ba jaruma Maryam Yahaya ba ce, tare da gano cewa wasu gurɓatattun mutane ne ke son amfani da wannan damar domin ɓata wa jarumar suna ta yadda su ka yi amfani da sunan jarumar tare da saka hotunan ta a kusa da bidiyon domin su ja hankalin masu kallo tare da kawo shakku da ruɗani a cikin al’umma.”

Ya kuma ƙara da cewa, “Mu na yin kira tare da gargaɗi ga masu irin wannan halayya ta ɓata wa al’umma suna, musamman ‘yan masana’antar Kannywood, da su kuka da kan su, domin duk wanda hukumar ta samu da irin wannan laifi, to babu shakka zai fuskanci fushin hukuma.

“Haka kuma mu na ƙara jaddada aniyar mu ta ƙara saka ido tare da hukunta duk wanda aka samu da laifin karya dokokin ba tare da sani ko sabo ba.”

Loading

Tags: baɗalabidiyoHukumar Tace Finafinai ta Jihar KanoKannywoodMaryam Yahaya
Previous Post

Tunda shirin fim ba mai gushewa ba ne nan kusa…

Next Post

Tinubu ya yabi Funke Akindele kan shirin ta na ‘A Tribe Called Judah’ da ya yi cinikin naira biliyan ɗaya

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Tinubu ya yabi Funke Akindele kan shirin ta na ‘A Tribe Called Judah’ da ya yi cinikin naira biliyan ɗaya

Tinubu ya yabi Funke Akindele kan shirin ta na 'A Tribe Called Judah' da ya yi cinikin naira biliyan ɗaya

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!