• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, July 3, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Marubuci Maizare ya kuɓuta daga hannun ɓarayi

by DAGA ABBA MUHAMMAD
March 17, 2020
in Labarai
0
Malam Abdullahi Yahaya Maizare

Malam Abdullahi Yahaya Maizare

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
SANANNEN marubucin nan kuma mashiryin finafinai, mazaunin Zariya a Jihar Kaduna, Malam Abdullahi Yahaya Maizare, a yau ya samu kuɓuta daga hannun ɓarayi masu garkuwa da mutane.
 
Hakan ya biyo bayan kuɗin diyya da iyalan sa su ka biya ɓarayin da ke riƙe da shi.
 
Majiyar mujallar Fim ta ce a yau Talata aka tsince shi magashiyan a wani wuri, amma majiyar ta shaida wa mujallar cewa ba ta san inda aka tsince shi ɗin ba domin a lokacin da iyalin sa su ka kira ta ba ta jin su sosai, domin su na ta kuka.
 
Sai dai matar sa ta ce ya dawo ba shi da lafiya, don ko magana ba ya iya yi, har an kwantar da shi a asibiti.
 
Idan kun tuna, a makon jiya mujallar Fim ta ba ku labarin yadda ɓarayin su ka sace Maizare a daren Asabar, 7 ga Maris, 2020 lokacin da ya je karɓo kuɗin hayar gidan wani maigidan sa a Sabon Garin Zariya.
 
Da farko ɓarayin sun buƙaci sai an biya naira miliyan N10 za su sako shi, daga baya su ka rage kuɗin zuwa miliyan 5, sannan kuma sai aka samu matsaya da su cewa rabin miliyan za a biya.
 
A shekaranjiya Lahadi ɓarayin su ka buga wa iyalin waya, su ka ce ranar Talata ce ƙarshe, ko a biya su kuɗin ko su kashe shi.
 
A jiya ɗan sa mai suna Abba ya kai masu kuɗin, waɗanda aka tara ta hanyar karo-karo.
 
Wasu daga cikin marubuta da kuma wasu membobin haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu shirya finafinai ta ƙasa, MOPPAN, su na daga cikin waɗanda su ka bada gudunmawar kuɗin diyyar.
 
Marubutan sun haɗa da Aunty Sadiya Kaduna, Fatima Ɗanbarno, Ibrahim Sheme, da sauran su.
 
Masu shirya finafinai kuma sun haɗa da shugaban MOPPAN na ƙasa, Dakta Ahmad Sarari da sakataren ƙungiyar, Al-Amin Ciroma, da shugabar ƙungiyar a reshen Jihar Kaduna, Hajiya Fatima Lamaj.

Loading

Previous Post

Ladi Mutukaraba ta rasu

Next Post

Lamaj ta kai wa Maizare gudunmawa a asibiti

Related Posts

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Next Post
Lamaj tare da Ɗanmaliki lokacin ziyarar su ga Maizare a asibiti

Lamaj ta kai wa Maizare gudunmawa a asibiti

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!