TSOHON Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Arewa (Arewa Film Makers Association of Nigeria, AFMAN) na Ƙasa kuma jarumi a Kannywood, Alhaji Abdullahi Sani (Baba Ƙarami) ya nuna ɓacin rai kan wani hoto da ake yaɗawa a kan sa a soshiyal midiya inda aka rubuta cewa ya yi nadamar shiga harkar fim.
A hoton, an nuno shi a kan keken guragu cikin wani yanayi na tsananin rashin lafiya.
Baba Ƙarami ya faɗa wa mujallar Fim cewa, “Wannan maganar sam ba gaskiya ba ce, don babu wata kafar yaɗa labarai da na yi hira da ita na faɗa musu wannan magana. Kawai dai wasu ne suka ƙirƙiri labarin don wata biyan buƙata tasu.”
Ya ƙara da cewa, “Wannan hoton da suke yaɗawa an ɗauke shi ne a wani sin da na fito cikin fim ɗin ‘Aliyah’, don haka ba hoto na ba ne na zahirin yadda nake, na cikin fim ne.”
A game da batun lafiyar sa kuwa, ya ce, “Na yi rashin lafiya a kwanakin baya har na kwanta a asibiti sakamakon ciwon hawan jini da nake fama da shi. Amma dai a yanzu na samu sauƙi, ina ci gaba da gudanar da harkokin da nake yi.
“Don haka waccan magana da ake yaɗawa ƙarya ce, kuma na ɗauki waɗanda suka yaɗa ta a matsayin maƙiya na.
“Don haka ina bai wa masoya na haƙuri sakamakon yadda hankalin su ya tashi saboda ganin labarin.
Ni ɗan fim ne kuma ina ci gaba da ayyukan da nake yi na fim ban kuma yi nadama ko da-na-sanin fim da nake yi ba.”
![]()






