Khadijatul Iman, ɗiyar jarumi kuma mawaƙi Sani Musa Danja da jaruma kuma furodusa Mansurah Isah, ta burge ɗimbin jama’ar da suka halarci ƙwarya-ƙwaryan bikin zagayowar ranar haihuwar ta a jiya Laraba.
Iman ta yi bikin ne a gidan mahaifin ta Sani Danja da ke unguwar Badawa a Kano, inda ƙawayen da ‘yan’uwa da abokan arzikin ta suka taru domin taya ta murna.
A wajen bikin dai an an shirya liyafar cin abinci, aka nishaɗantar da mahalarta waƙoƙi tare da raba kyaututtuka na musamman ga jama’a.
Ita ma Khadijatul Iman ta samu kyaututtuka daga ƙawaye da ‘yan’uwa da suka kawo mata don taya ta murna.

An tashi daga taron da magariba inda Khadijatul Iman ta yi godiya ga Allah da ya nuna mata wannan rana.
Ta yi godiya ga iyayen ta bisa kulawar da suke ba ta, sannan ta gode wa dukkan jama’ar da suka taru domin taya ta murna.
![]()







