A YAU Alhamis, tsohuwar jarumar Kannywood, Hajiya Fati Ladan, ta shirya wa ƙaramar ‘yar ta Raliya (Ihsan) bikin murnar zagayowar ranar haihuwar ta, inda ta cika shekara ɗaya a duniya.
An gudanar da bikin a farfajiyar gidan su da ke Yerima Close, kan Titin Jinya, daura da Titin Kanta, Kaduna.
Bikin, wanda aka fara da misalin ƙarfe 5:00 na yamma, ya samu halartar ƙawayen Fati da kuma matan abokan mijin ta, Alhaji Yerima Shettima, da ‘ya’yan su.
Da yake bikin na yara ne, mai gabatarwa, wato kakakin magana (MC), Ibrahim Alhassan, ya gabatar da gasar rawa a tsakanin yaran inda ake kiran namiji ɗaya, mace ɗaya a saka masu waƙa su yi rawa. Wanda ya fi iya wa, shi ne zakaran.
Sai dai fa mata sun ba maraɗa kunya, domin su ne suka lashe gasar da kusan kashi 95 cikin ɗari, ciki har da babbar ‘yar Fati, Humaira.
Bayan nan, sai kuma aka shiga fagen goge wuya, cin maƙulashe, inda kowa ya ci gasashhen naman rago da sauran abubuwan sha.
Daga nan kuma sai aka yanka kek tare da yin hotunan Ihsan da mahaifiyar, yara da kuma iyayen su.

Bayan kammala hotunan ne Fati Ladan ta yi jawabin godiya ga dukkan mahalarta taron inda ta ce, “Ina godiya matuƙa da irin ƙaunar da kuke nuna min. A duk lokacin da zan yi abu, kuna ƙoƙarin halarta. Na gode sosai. Allah ya maida kowa gidan sa lafiya.
“Iyayen yara da yara sun nuna farin cikin su da wannan bikin, domin sun cashe sosai.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa an haifi Raliya a ranar Talata, 5 ga Nuwamba, 2024, a asibitin sojojin sama (Air Force Base) da ke Mando, Kaduna.
Allah ya raya Raliya, ya albarkaci rayuwar ta.

![]()







