FITACCIYAR jaruma Ummi Ibrahim (Zee-Zee) ta bayyana abin da ya sa aka ce wai ta mutu.
A sabon rubutun da ta yi a Instagram tare da hoto mai nuna ta kwance a kan gado a matsayin mara lafiya, Zee-Zee ta nanata cewa wai ta faɗi ta suma ne a Kaduna, wanda hakan ya sa ƙawar ta ta tura saƙon cewa ta mutu.
Mutane da dama sun ƙaryata wannan kalamin nata.
Ga abin da ta rubuta ɗin, ba tare da mujallar Fim ta gyara nahawun rubutun nata ba:
“Salam to nigerians sunana UMMI IBRAHIM ZEEZEE ,ina mai baku hakuri dangane da labari da kukaji mai tada hankali na cewa na MUTU .to da raina ban mutu ba kawai dai na yanki jiki ne na fadi na suma a gidan wata kawata a garin kaduna to sai tayi zaton ko na mutu ne dan tayi ta zuba min ruwa ban farfado ba ,shine tayi posting ta gayawa duniya cewar na mutu har sai da mijinta ya kaini asibiti likita ya auna ni ya gano cewa da raina ban mutum ba .saboda haka duk Wanda ya nuna damuwarsa dayaji zancen mutuwana to ina godiya da kaunarsa a gare ni .saboda haka inan da raina saidai banda lafiya ne seriously domin depression (damuwa) yana damuna sosai dan haka masoyana ku tayi da addu’ar samun lafiya nagode allah yasa mun shiga cikin watan ramadan lafiya ubangiji yasa muga karshensa lafiya sannan allah ya karbi ibadun mu na wannan wata mai alfarma amin thank you all for your love, concern , and caring toward me #asha ruwa lafiya”.







