• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ummi Zee-Zee ta dawo gida ‘lafiya lau’

by DAGA IRO MAMMAN
April 13, 2021
in Labarai
0
Ummi Zee-Zee ta dawo gida ‘lafiya lau’
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCIYAR jarumar finafinan Hausa, Ummi Ibrahim (Zee-Zee), ta dawo gida a jiya, a ranar da ake sa ran za a kawo gawar ta kamar yadda wani ya yi iƙirari.

Wata ƙwaƙƙwarar majiya mai kusanci da jarumar ce ta faɗa wa mujallar Fim hakan a daren jiya.

Majiyar ta ce Zee-Zee ta dawo gida ne a jiya Litinin, “kuma lafiyar ta ƙalau”.

Sai dai kuma majiyar ba ta yi ƙarin bayani ba, illa dai ta ce mu jira zuwa yau.

A yau ɗin kuma sai majiyar ta ce, “A dai faɗa wa duniya cewa Ummi ta dawo, kuma lafiyar ta ƙalau.

“Kuma in-sha Allahu zuwa anjima za mu sanar da ku abin da ya faru. Sai dai babu shakka yanzu haka ta na gida, kuma lafiyar ta ƙalau.”

Idan kun tuna, a shekaranjiya ne labari ya yaɗu cewa wai jarumar ta rasu a gidan wata ƙawar ta a Kaduna.

Amma wata hukumar tsaro da mujallar Fim ta tuntuɓa a Kaduna kan lamarin ta gano cewa wayar Zee-Zee ta na cikin yankin Sabo Garin a birnin Kano.

Haka kuma binciken da rundunar ‘yan sanda ta Jihar Kaduna ta yi ya gano babu wata gawa da aka samu a jihar da sunan ta Zee-Zee ce.

Abin da ya ɗaure wa mutane kai shi ne yadda aka tura saƙon ‘mutuwar’ ta hanyar wayar Zee-Zee ɗin da sunan wata ƙawar ta wai Khairat.

Amma Hasina Ɗan-Chaina, ƙanwar Zee-Zee da ke aure a Jos, ta bayyana cewa ita dai a iya sanin ta babu wata ƙawar Zee-Zee mai wannan sunan.

Tun a ranar da abin ya faru dai Hasina ta bayyana tababa game da mutuwar da aka ce yayar ta ta yi.

Yanzu kuma da Zee-Zee ta dawo gida, mutane za su ci gaba da tambayar me ya faru har aka tura saƙo ta hanyar wayar ta cewa ta rasu.

Wasu tambayoyin su ne: shin wanene ya tura saƙon? Wace manufar ake so a cimmawa? Ina Zee-Zee ta je ta kwana a daren Lahadi? Ya aka yi ta dawo gida? 

Wasu tambayoyin su ne: ina mutumin nan da ya riƙa kiran su Hasina Ɗan-Chaina ya na cewa shi ɗan sanda ne, wai gawar Zee-Zee na hannun sa, kuma wai za su kai gawar gidan su jarumar a jiya? Me ya sa ba su kai gawar ba?

Ana sa ran kila nan da wani lokaci Zee-Zee da kan ta za ta fito ta amsa wa jama’a waɗannan tambayoyin.

Duk wannan badaƙalar dai ta faro ne daga ranar 3 ga Afrilu, 2021 lokacin da Zee-Zee ta tura saƙo a Instagram cewa ta yanke shawarar za ta kashe kan ta.

Washegari kuma ta fito ta ce wani Ibo ne ya damfare ta kuɗi har naira miliyan 450, wanda hakan ya haifar mata da ciwon damuwa (depression) har ta ji gara ma ta mutu ta huta.

Mutane da dama sun soki jarumar kan wannan badaƙalar, su na cewa ita ce ta kitsa ta, kuma ta na yi ne domin ta ɗau hankalin jama’a, ba wai don gaskiya ba ce.

Wasu kuma sun ce ciwon damuwa da gaske ne, don haka sun yi addu’ar Allah ya ba ta lafiya.

Wani hoto da Zee-Zee ta ɗora a shafin ta na Instagram tare da kalma ɗaya, ‘Sick’, jim kaɗan bayan wallafa labarin mu. Hoton na nuna an yi mata ƙarin ruwa, kuma kalmar na nufin, ‘Rashin lafiya’.
Tags: depression in Nigeriahausa actresshausa filmsKannywoodUmmi Zee-Zee
Previous Post

Ramadan Mubarak!

Next Post

Cewar Zee-Zee: Abin da ya sa aka ce na mutu

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Cewar Zee-Zee: Abin da ya sa aka ce na mutu

Cewar Zee-Zee: Abin da ya sa aka ce na mutu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!