• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ban ga imani ga malaman Nijeriya ba, inji Zee-Zee

by DAGA IRO MAMMAN
April 30, 2021
in Labarai
0
Ban ga imani ga malaman Nijeriya ba, inji Zee-Zee
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCIYAR jarumar Kannywood, Ummi Ibrahim (Zee-Zee), ta bayyana cewa ita dai ba ta ga cikar imani a wajen malaman Musulunci na Nijeriya ba, domin kuwa babu wani daga cikin su da ya kira ta ya yi mata nasiha a kan iƙirarin kashe kan ta da ta ce za ta yi kwanan baya, maimakon haka sai tsina da zagi.

Zee-Zee ta bayyana haka ne a wani saƙo da ta tura a Instagram a yau bayan ziyarar da ta kai wa Kwamishinar Harkokin Mata ta Jihar Kano, Dakta Zahra’u Muhammad, bisa gayyatar ita kwamishinar.

Ta tuno da cewa a lokacin da ta yi barazanar kashe kan ta ɗin, babu malamin da ya fito ya yi mata nasiha.

Ta ce: “In ban da zagi da na ke sha a gun jahilai babu wani babba ko babban malami daga malaman Nijeriya da ya kira ni ya min nasiha sai ita (kwamishinar).”

Mujallar Fim ta ruwaito tsohuwar jarumar ta na faɗin, “Da a ce na kashe kan nawa, to da manyan malaman Nijeriyan ba wanda ba zai hau mumbari ya tsine min ba saboda a ce su masu imani ne bayan kuma ni ban ga imanin ba. Don da akwai imanin, to da sun kira ni sun min nasiha a kan batun kashe kai na da na ce zan yi!

“Wallahi ko a Saudiyya ne, ina Musulma in furta kalmar zan kashe kai na, to da har limamin Harami sai ya kira ni ya min nasiha. Amma mu namu malaman ba ruwan su da rayuwar mu; rayuwar ‘ya’yan su ce kawai ta dame su, ba rayuwar ‘ya’yan wasu ba, bayan kuma Manzon Allah s.a.w. amana ya bar mu a gun su domin su zame mana gata, su dinga sa mu a hanyar shiriya da nasiha.”

A game da ziyarar da ta kai wa kwamishinar, Zee-Zee ta ce, “Na je mun zauna, ta min nasiha ne  sosai mai ratsa jiki dangane da maganar ‘suicide’ da na ce zan kashe kai na.”

Ta ce ta faɗa wa kwamishinar matsalolin da su ka sa ta ce za ta kashe kan ta.

“Shi ne ta min alƙawarin share min hawaye na, ta kuma ci alwashin ba wanda zai sake take ni ya kwana lafiya a Nijeriya sai ta bi min haƙƙi na domin ita mace ce wanda ta ke kare haƙƙin rayuwar ɗan’adam, musamman mata, domin mata ta ke wakilta,” inji ta.

Zee-Zee ta ce bayan Malama Zahra’u ta gama yi mata nasiha, ta kuma kai ta gidan da gidauniyar ta ta ke inda ta ga yara marayu maza da mata da ta ke riƙo. 

“Wallahi ban san lokacin da na fashe da kuka ba domin ni na daɗe ban ga mace mai imani da sanin darajar rayuwar ɗan’adam ba irin Malama Zahra’u,” inji ta.

Zee-Zee ta na cike da godiya ga kwamishinar saboda wannan “nasiha mai ratsa jiki” da ta yi mata.

Ta ce, “Ina godiya ta musamman zuwa ga kwamishinan, Malama Zahra’u, dangane da yadda ta nuna damuwar ta har ta buƙaci in zo ta ji matsalar da ta sa na ke son kashe kai na.” 

Ta ƙara da cewa, “Sannan a da ban taɓa zaton a jam’iyyar APC akwai mutane masu imani irin na Malama Zara’u ba. To gaskiya daga yau zan fara girmama duk wani ɗan jam’iyyar APC saboda darajar karamci da ta min, ta kuma ce jahilci ne Musulumi ya ce zai kashe kan sa amma a hau zagin sa maimakon a yi maza a hana shi aikatawa, a kuma yi masa nasiha.

“Ina sake godiya Dakta Malama Zara’u. Allah Ubangiji ya yafe miki zunuban ki tun ki na raye, ya kuma biya miki buƙatun ki na duniya da lahira, sannan ya ba ki Aljanna Fiddausi, amin.”

Loading

Previous Post

Tsohon jarumi Ibrahim Mu’azzam ya kwanta dama

Next Post

Buhari ya sake naɗa Adedayo Thomas muƙamin shugaban Hukumar Tace Finafinai

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Buhari ya sake naɗa Adedayo Thomas muƙamin shugaban Hukumar Tace Finafinai

Buhari ya sake naɗa Adedayo Thomas muƙamin shugaban Hukumar Tace Finafinai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!