SHUGABAN Ƙasa Muhammadu Buhari ya sabunta naɗin Alhaji Adedayo Thomas a matsayin Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Bidiyo ta Ƙasa (National Film and Video Censors Board, NFVCB).
Bayanin naɗin ya fito ne a cikin wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Malam Garba Shehu, ya raba a yau 30 ga Afrilu, 2021.
A sanarwar, wadda mujallar Fim ta samu kwafen ta, Buhari ya ba Thomas damar ci gaba da shugabantar hukumar na tsawon shekara huɗu.
An sabunta wa’adin nasa tare da na wasu hukumomin gwamnati da su ka haɗa da NTDC da NCAC da kuma ‘National Troupe of Nigeria’.
Shi dai Alhaji Adedayo Thomas, Buhari ya fara naɗa shi shugabancin NFVCB ne a ranar 30 ga Maris, 2017.
Kafin naɗin nasa, ɗan jarida ne wanda ke aiki a matsayin mai bada shawara na musamman ga Shugaban Hukumar Yaƙi da Fataucin Muggan Ƙwayoyi, wato NDLEA, kuma shi ne shugaban wata ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam mai zaman kan ta mai suna ‘African Liberty Organisation for Development’ (ALOD).
![]()







