MASU harkar shirya fim a Nijeriya sun yi wani babban taro jiya a Legas kan yadda za a daina nuno shan taba ko tallar ta a finafinan da ake yi a ƙasar.
Wata ƙungiya mai suna KAPA ce ta shirya taron, wanda aka yi a wani otal mai suna De Rembrandt da ke unguwar Ikeja, kuma manyan masu shirya finafinai daga sassan Nijeriya daban-daban ne su ka halarta.
Taken taron dai shi ne “Stakeholders’ Summit on Smoking in Movies”.
Daga masana’antar shirya finafinai ta Kannywood, mutum biyu su ka samu halarta, wato Hajiya Fatima Ibrahim Lamaj da Alhaji Maikuɗi Cashman; a yayin da Lamaj ta wakilci shugabar Ƙungiyar Matan Kannywood (K-WAN), Hajiya Hauwa A. Bello, wadda ita Lamaj ɗin ce mataimakiyar ta, shi kuma Cashman ya wakilci shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai Ta Nijeriya (MOPPAN), Dakta Ahmad Sarari.
Da mujallar Fim ta tambayi Lamaj yadda taron ya gudana, sai ta ce, ”Wannan taro an yi shi ne kan shaye-shayen taba sigari da kuma illar da ita kan ta tabar ta ke yi wa masu shan ta.
“Magana ta gaskiya, taron ya yi armashi sosai, saboda an nuna mana yadda taba sigari ke da illa ga ɗan’adam, kuma da yadda bai kamata mu na sanya ana shan taba a fim ba, domin duk fim ɗin da aka saka taba sigari a ciki Hukumar Tace Finafinai ba za ta tace shi ba.”

Ta ce ita kan ta ta nuna wa mahalartan taron wani fim da ta shirya kan illar shaye-shaye ga al’umma, wanda ya taɓo har da ita sigarin. Ta ce a fim ɗin an nuna yadda saboda shaye-shaye har wani mutum ya yi wa ƙaramar yarinya ‘yar makaranta fyaɗe.
Lamaj ta ce mahalartan taron sun ce tunda shaye-shayen ne ya yi jagoranci ga aikata haka ɗin za a iya kauda kai, “amma kuma sai na sa ‘Cigaratte Is Dangerous To The Health’ kamar yadda ake rubutawa a finafinan ƙasashen waje.”
Ta bayyana cewa an sanar da su cewa duk mashiryin fim wanda ya karɓi tallar taba, zai biya diyyar naira miliyan biyar.
A cewar ta, “Ire-iren waɗannan batutuwa duk su aka tattauna a kai a wurin taron domin su ne maƙasudin shirya taron.”
Babbar furodusar, wadda kuma ita ce shugabar Ƙungiyar Furodusoshi ta Jihar Kaduna, ta faɗa wa mujallar Fim cewa, “Ina kira ga mutanen mu da su bi dokokin gwamnati, don ba ka isa ka yaƙi gwamnati ba. Saboda akwai waɗansu da su ka yi magana a wurin a kan cewa ai ba gwamnati ke ba su kuɗi ba, sai aka ce masu, ‘Gwamnati ba ita ke ba ku kuɗi ku yi fim ba, amma gwamnati na da dama ta ce in ka yi fim da ka saɓa wa dokokin ta za ta iya cin tarar ka. Don haka dole ne mutum ya bi dokoki da ƙa’idojin gwamnati.’
“Don haka ina jan hankalin mutanen mu da su bi umarnin gwamnati; in aka ce ka yi, ka yi, in aka ce ka bari, ka bari.”


![]()







