• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Martani: Rikici tsakanin ‘yan fim da ‘yan jarida a kan ‘Labari Na’

by DAGA ABDUSSALAM BARISTA HOTORO
September 11, 2021
in Tsokaci
0
Naziru M. Ahmad (Sarkin Waƙa)

Naziru M. Ahmad (Sarkin Waƙa)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

WASU ‘yan jarida sun koka kan yadda su ka yi tunanin an ci zarfin ɗan jarida a cikin fim mai dogon zango mai suna ‘Labari Na’. 

A cikin kashi na 11 a zango na uku an nuna ɗan jarida na neman ba’asi a wajen fitaccen mawaƙi Naziru M. Ahmad (Sarkin Waƙa) dangane da rayuwar Sumayya (Nafisa Abdullahi) wanda ya jaddada ita ya kamata a tuntuɓa kasancewar rayuwar ce. A yayin da ɗan jarida ya dage wajen bibiyar labari sai Naziru ya nemi a ba wa ɗan jaridar kuɗin mota don ya yi na mota, alamun ba zai iya samun amsar tambayar da ya ke nema daga gare shi ba.

Masu da’awar an wulaƙanta ɗan jarida a wannan shirin sun yi ta kiran lambar daraktan fim ɗin, Malam Aminu Saira, don jin ta bakin sa. 

Marubucin wannan shiri, Nasir Gwangwazo, tsohon ɗan jarida ne da ya ɗauki tsawon shekaru ya na aikin jarida a babbar jaridar ‘Leadership A Yau’, wanda har matsayin babban edita ya riƙe, kuma yanzu haka ma shi ne editan jaridar ‘Manhaja’ da kamfanin Blueprint ke wallafawa. Shin zai yi wani abu ne don muzanta aikin sa da ya ke cin abinci da shi? Ba mamaki ya san akwai ‘yan jarida da su ke zubar da mutuncin aikin su wajen yawon maula da roƙo, shi ne ya rubuta hakan don jan hankalin su a kan riƙe mutuncin kan su.

Ko a kwanakin baya an samu taƙaddama tsakanin ‘yan jarida a Kano inda wani babba daga cikin su ya soki masu irin wannan hali na yi wa ‘yan siyasa maula da tumasanci. Kuma kamar yadda a kowane sashi na rayuwa a kan iya samun nagari da na ƙwarai, su ma ‘yan jarida ba mala’iku ba ne da za a ce babu nagari da na banza a cikin su.

Kamfanin Saira Movies ne ya shirya fim ɗin ‘Malika’ a shekarun baya da har gobe babu wani fim a masana’antar Kannywood da ya fito da ƙima da darajar aikin jarida sama da shi. An nuna babban jarumi da ake yi wa laƙabi da Sarkin Kannywood a matsayin ɗan jarida mai tsattsauran ra’ayi a kan kiyaye dokokin aikin jarida. Fim ɗin, marubuci kuma ɗan jarida Maje El-Hajeej Hotoro ya rubuta shi, kuma shi ma Maje babban ɗan jarida ne, wanda ya ke da gogewa a kan aikin jarida. Shin ko sauran ‘yan jarida sun yi masa rubutun yabo a kan wannan gagarumin aiki? 

‘Malika’ ya yi tashe da shaharar da ya kamata ‘yan jarida su yi kishin aikin su wajen yaɗa shi ko yin rubutun yabo ga kamfanin a matsayin ƙarfafa gwiwa, amma babu wata rubutacciyar shaidar yin hakan, sai yanzu su ka ga an yi musu ba daidai ba. Shin me ‘yan jarida su ke so? Ba a ba wa wasu ‘yan jarida na goro ne ko kuwa su ba sa ganin aikin alheri ne sai an taɓa su?

* Abdussalam Barista Hotoro ya rubuto ne daga Kano

Copyright © Fim Magazine. All rights reserved.
www.fimmagazine.com

Loading

Tags: Ali Nuhu Sarkin KannywoodAminu SairaArewa24 TVhausa filmsKannywoodLabari NaMaje El-Hajeej HotoroMalikaNasiru GwangwazoNaziru M. AhmadNaziru Sarkin WakaNigerian journalists
Previous Post

Buri ya cika, Rahama Sadau ta zama jarumar finafinan Indiya

Next Post

Naziru Sarkin Waƙa ya hayaƙa ‘yan jarida

Related Posts

Aure Da Saki A Fim: Gangan Ko Gaske?
Tsokaci

Aure Da Saki A Fim: Gangan Ko Gaske?

March 7, 2025
‘Arewa Republic’. Kun gani ba?
Tsokaci

‘Arewa Republic’. Kun gani ba?

February 10, 2025
Rukuni huɗu na masu kallon fim ɗin Hausa
Tsokaci

Rukuni huɗu na masu kallon fim ɗin Hausa

February 7, 2025
Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na
Tsokaci

Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na

September 1, 2024
Dakta Aliyu U. Tilde
Tsokaci

Arewa: Tsakanin Ilimi Da Sana’a

June 12, 2024
Gwamna Abba Kabir Yusuf
Tsokaci

Shawara ga Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

June 10, 2024
Next Post
Naziru Sarkin Waƙa

Naziru Sarkin Waƙa ya hayaƙa 'yan jarida

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!