ƘUNGIYAR Matan Kannywood (Kannywood Women Association of Nigeria, K-WAN) ta ba fitaccen mawaƙi Naziru M. Ahmad wa’adin kwana uku da ya janye ƙazafin da ya yi wa mata ‘yan fim ko kuma su yi ƙarar sa a kotun Musulunci.
Wa’adin ya fara aiki ne daga yau Litinin, 14 ga Fabrairu, 2022.
Shugabar ƙungiyar, Hauwa A. Bello (Edita), ita ce ta bada wa’adin a cikin wata takardar sanarwa da ta aika wa mujallar Fim.
Naziru M. Ahmad, wanda ake wa laƙabi da Sarkin Waƙa, ya wallafa wani bidiyo a soshiyal midiya inda ya yi iƙirarin cewa ba a sanya jarumai mata a fim a masana’antar Kannywood sai sun bada kan su an yi zina da su.
Ya yi maganar ne domin bada martani ga waɗanda su ka yi fatali da iƙirarin da dattijuwar ‘yar wasa Hajiya Ladin Cima (Tambaya) ta yi inda ta ce ba a taɓa biyan ta sama da N5,000 ba idan ta yi fim.
Naziru ya zaɓe jarumai Ali Nuhu da Falalu Ɗorayi musamman a martanin sa, ya ce babu tsoron Allah a zuciyar ‘yan fim.

Maganar tasa ta janyo surutai sosai, kuma ta zama makami ga mutane masu adawa da harkar fim a yayin da kuma ta hayaƙa wasu ‘yan fim ɗin.
A takardar da ta rattaba wa hannu a yau, Hauwa Edita ta ce, “Duba da abin da ya faru wanda Naziru M. Ahmad ya yi wasu kalamai na cin zarafi ga mata masu sana’ar fim, mu na kira a gare shi da ya janye kalaman sa cikin kwana uku daga yau, in kuwa bai yi haka ba za mu kai shi kotun Musulunci bisa tuhumar ya yi mana ƙazafi.”
Tun da fari, kwana kaɗan kafin wannan sabon matakin da ƙungiyar ta ɗauka, sai da Hauwa Edita ta yi Allah-wadai da kalamin mawaƙin a wata sanarwa da ta raba wa manema labarai.
A sanarwar, ta ce, “A madadin shigabanci na ƙungiyar mata ta ‘Kannywood Women Association’ mu na tir da Allah-wadai da wasu kalamai da Naziru Sarkin Waƙa ya yi a kafar sadarwa kan wasu munanan halaye da ya danganta mata ‘yan fim da su, wanda wannan ƙazafi ne kuma ɓata suna ne da taɓa martabar wasu daga cikin ‘yan wannan masana’anta.
“Mu na kira ga Naziru ya nemi gafara don ya shiga haƙƙin mu.
“Allah ya ci gaba da kare wannan masana’anta. Allah ya kare mutuncin mu da martabar mu, amin.”