DUKKAN godiya ta tabbata ga Allah (SWT). Kamar yadda mu ka sanar da ku za a ɗaura auren editan mujallar Fim, wato Abba Muhammad, da sahibar sa Jamila Ibrahim Dassi, cikin yardar Allah an ɗaura auren kamar yadda aka tsara.
An ɗaura auren a ranar Juma’a, 4 ga Yuni, 2021 da misalin ƙarfe 1:40 na rana, bayan an idar da sallar Juma’a, a masallacin Sheikh Ja’afar Mahmud Adam da ke Unguwar Dosa, Kaduna, a kan sadaki N70,000.
Ɗimbin jama’a da su ka halarci ɗaurin auren sun haɗa da ‘yan siyasa kamar su tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Mahmud Aliyu Shinkafi, Honarabul Mukhtar Isah Hazo (baban amarya), Dakta Auwal Abdullahi Aliyu (waliyyin amarya, ɗan majalisa mai wakiltar Zariya da Kewaye, Honarabul Ahmad Muhammad Chokali, ɗan majalisar Jihar Kaduna mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Sanga, Honarabul Halliru Gambo Dangana, da sauran su.

A ɓangaren iyayen ango akwai mahaifin ango, Malam Muhammad Aliyu Giɗaɗo, da Malam Shehu Mu’azu (wakilin ango), Malam Lawal Muhammad Giɗaɗo, Malam Yakubu Aliyu Giɗaɗo da Malam Nasiru Muhammad Giɗaɗo.
Sauran manyan baƙi da ‘yan fim sun haɗa da Alhaji Kabiru Assada, Malam Rabi’u Yunus Agege, Malam Aliyu A. Gora II, Malam Shafi’u Usman Namaigero, Mista Akintunde Adebayo, Isah Bawa Doro, Ɗayyab Maiɗa’a, Ibrahim Al-Imash, Ahmad Yariman Tiga, Abdulrahmna Ɗan Gwal, Ɗanladiyo Mai Atamfa, Lawal Mai Atamfa, Nafi’u Bigi, Muhammad S. Yaro, Ibrahim Baba Iro, Muhammad Busra, Hamza Isah Ahmad, Mubarak Sa’id, Ibrahim Sani, Abdurasheed Muhammad, Abdullahi Abu Uku, Nuhu S. Aliyu, Usman A.A. Rasheed, A.A. Rasheed Kabala, Adamcy Khan, Auwal Yahaya DG, Ibrahim 2-Effects Isma’il I.E.C., Rabi’u Gamji, Salisu Dage, Yusuf Muhammad, Ibrahim Ɗanguziri, Modibbo Muhammad, da sauran su.

Kafin ranar ɗaurin auren dai an gudanar da shagulgula kamar haka:
* Ranar Ƙauyawa (Ƙauye Day) – Litinin, 31 ga Mayu inda amarya da ƙawayen ta su ka yi shiga irin ta ‘yan ƙauye, su ka ci dambu da su magaryar da sauran kayayyakin gargajiya;
* Wankan Amarya (Bridal Shower) – Talata, 1 ga Yuni, inda aka yi biki, shi ma na amarya da ƙawayen ta;
* Gasar ƙwallon ƙafa – Laraba, 2 ga Yuni, wadda aka yi a filin wasa na Ahmed Musa Neighbourhood Centre da ke Sabon Hanya, unguwar Kamazo, Kaduna.

An buga gasar tsakanin ‘yan gidan ango da ‘yan gidan amarya, inda aka tashi 3-3.
Ango da abokan sa sun halarci wurin, haka ita ma amrya da ƙawayen ta;
* Kamu – Alhamis, 3 ga Yuni, inda aka yi biki a gidan su amarya da ke Legistilative Quarters, Kaduna. An fara bikin da misalin ƙarfe 5:00 na yamma, inda ango da amarya su ka shiga filin taron, aka umarce su da su zauna a inda aka tanadar masu.

Da farko an buɗe taro da addu’a, daga nan kuma aka shiga abin da ya tara jama’a a wurin. An kira amarya da ango tsakiyar fili don su taka rawa a gaban ‘yan’uwa da abokan arziki. Bayan sun koma sun zauna kuma, sai aka kira Ɗanladiyo Mai Atamfa tare da Nafeesa Yahaya Maiyaƙi, su ka nishaɗantar da taron da waƙar da su ka yi wa ango da amarya.
An ci gaba da shagali har zuwa ƙarfe 8:00 na dare, inda a wannan lokaci ne aka sallami kowa.

Wasu daga cikin waɗanda su ka halarci bikin sun haɗa da Dakta Auwal Abdullahi Aliyu, Ibrahim Al-Imash, Musa Mairabo, Isah Bawa Doro, Agga Bawan Mata, Murtala Darakta, Salisu Dage, Ɗanladiyo Mai Atamfa, Muhammad S. Yaro, Muhammad Busra, Ibrahim Baba Iro, Hamza Isah Ahmad, Ahmad Yariman Tiga, Nafeesa Yahaya Mai Yaƙi, A.A. Rasheed Kabala da sauran su.
* Ɗaura Aure – Juma’a, 4 ga Yuni. Bayan an ɗaura auren da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, an yi bikin Ranar Iyaye Mata (Mothers Day). Da misalin ƙarfe 7:00 na yammna kuma aka ɗauki amarya zuwa ɗakin mijin ta da ke unguwar Kinkinau, Kaduna.
Mu na fatan Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba, amin.




