• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Abin da ya sa tsohuwar jarumar Kannywood Halisa Muhammad take neman agaji

by ABBA MUHAMMAD
March 27, 2024
in Labarai
0
Abin da ya sa tsohuwar jarumar Kannywood Halisa Muhammad take neman agaji

Hajiya Halisa Muhammad Abdullahi... kafin ta shiga matsala

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

TSOHUWAR jaruma a Kannywood, Hajiya Halisa Muhammad ta na neman taimakon al’umma da su taimaka mata da kuɗi ko kuma saya mata allura da za a riƙa yi mata saboda jinyar da ta ke fama da ita ta sankarar mama (breast cancer).

Allurar za a yi mata ita ce har sau goma sha takwas, kuma duk ƙwaya ɗaya kuɗin ta ya kai N335,000.

An ga jarumar cikin wani bidiyo a soshiyal midiya inda ta ke neman taimako da kan ta. A ciki ta na cewa, “Assalamu alaikum wa rahamatullah. Suna na Halisa Muhammad. Ni ce mai fama da ciwon ‘breast cancer’, wato kansar mama kenan, na ke neman muhimmin taimako a wurin ku bayin Allah na wata muhimmiyar allura, kuma kuɗin ta na da tsada sosai, na ke neman taimakon ta a wurin ku bayin Allah.

“Allurar ta kan kai N335,000 duk ƙwara ɗaya. Kuma allurar nan za a yi ta sau goma sha takwas; round goma sha takwas za a yi min ita.

“‘yan’uwa da abokan arziki sun yi bakin ƙoƙarin su a kan ciwon nan. Kansa na da wahalar sha’ani, shi ya sa na fito na nemi taimakon ku, bayin Allah, ku ma ku taimaka min da kuɗin allurar nan ko allurar, kuma ina barar addu’o’i.

“Ubangiji Allah ya ba mu lafiya, ya kuma ba da ikon taimakawa.

“Zan aje akawun lamba ɗi na da kuma lambobin wayoyi na, duk wanda Allah ya ba shi iko ya taimaka mana da kuɗin allurar ko allurar. Allah ya ba ku iko, na gode sosai.”

Halisa a cikin bidiyon neman agaji

Halisa ta ɗauki tsawon lokaci ta na fama da wannan jinya, wanda har ta kai ga a watannin baya abokan sana’ar ta ‘yan fim sun tara mata kuɗi don fitar da ita ƙasar waje neman magani.

Kuɗin bai kai adadin da ake nema ba, don haka dole sai a gida aka yi mata aikin a wani asibiti a cikin garin Kano.

Tun a shekarar da ta gabata mujallar Fim ta so ta tattauna da ita a kan rashin lafiyar, sai dai kuma ita Halisar ta ƙi amincewa, ta roƙe mu da kada ma mu ba da labarin halin da ta ke ciki.

Sai dai a kwanan baya mun ba ku labarin ziyarar da wasu daga cikin abokan sana’ar ta su ka kai mata, wato ‘yan guruf ɗin Kannywood Family, a ƙarƙashin jagorancin tsohuwar jaruma Hajiya Hindatu Bashir da su mawaƙi Muddassir Ƙassim.

Bayan tura bidiyon neman taimakon da Nura Mado ya yi a cikin guruf ɗin, da dama sun tofa albarkacin bakin su a kan cewa ya kamata waɗanda su ka samu dama a cikin gwamnatin Kano irin su Abba El-Mustapha, Sanusi Oscar 442 da Fauziyya D. Sulaiman su taimaka su yi wa Gwamna Abba Kabir Yusuf magana ko za a dace.

Daga baya ita Halisar ta tura wani saƙo a Facebook da kuma cikin guruf ɗin da cewa, “Alhamdu lillah, mu na ganin ƙauna”. Sannan ta rubuta, “Allah ya saka da gidan Aljanna, Allah ya sa a mizani.”

Ga dukkan wanda ke son ba da nasa taimakon, ga lambar asusun ta na banki:

Lambar asusu: 0006710251

Banki: Jaiz Bank.

Suna: Halisa Muhammad Abdullahi

Allah ya sa a dace, amin.

Loading

Tags: agajiHalisa Muhammedkansar mamarashin lafiya
Previous Post

Kotu ta haramta wa Murja Kunya shiga soshiyal midiya 

Next Post

Sadiqu Artist ya zama baban Halimatus Sadiya

Related Posts

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Next Post
Sadiqu Artist ya zama baban Halimatus Sadiya

Sadiqu Artist ya zama baban Halimatus Sadiya

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!