• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Adam A. Zango: Na yi hijira zuwa Legas don in ceci rayuwa ta

by DAGA IRO MAMMAN
December 21, 2019
in Labarai
0
Adam A. Zango

Adam A. Zango

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

* ‘Ba abin da ya rage a Kannywood sai zalunci da sharri da cin mutunci’

 * ‘Zan maida iyali na Legas nan da wata 6’

 ADAM A. Zango ya bayyana cewa ya koma Legas da zama saboda harkar fim da waƙa ta ruguje a Arewa.

 Haka kuma ya ce nan da watanni shida ko sha-biyu masu zuwa zai ɗauke iyalin sa kacokam daga Kaduna ya mayar da su Legas.

 Ya ce zai yi hakan ne domin shi fa yanzu ya bar harkar finafinan Hausa kwata-kwata, ya koma Legas da zama domin gudanar da sana’ar waƙa.

 A hirar da ya yi da jaridar mako-mako ta Aminiya wadda aka buga a jiya Juma’a, shahararren jarumin kuma mawaƙi ya ce, “Na fara harkoki na (a Legas), komai ya kankama. Ina shirin cikin wata shida zuwa shekara ɗaya zan dawo da iyali na gaba ɗaya nan Legas, har da mahaifiya ta, cikin yardar Allah.”

 A hirar, wadda wakilin jaridar ya yi da shi a garin Legas ɗin, Zango ya bayyana cewa tunda ya kai ƙololuwa a harkar fim a Arewa, to abu mafi a’ala gare shi shi ne ya koma Kudu da zama domin harkokin sa za su fi ci a can.

 Ya ce, “Kamar ɗalibin ilimi ne da ya kammala karatun sakandare; idan ya na so ya ci gaba da karatu sai ya tafi makarantar gaba da sakandare ko ya je jami’a.”

 Wani dalilin da jarumin ya bayar kuma shi ne Legas gari ne inda ake samun kuɗi sosai.

 “Legas gari ne na samun rufin asiri,” inji shi. “Idan mutum na so ya samu rufin asiri mai nauyi, to Legas zai nufa.” 

Jarumin ya bayyana baƙin cikin sa kan yadda al’amurran sana’ar fim da waƙa su ka sukurkuce a Arewa. 

Ya ce: “A yanzu a arewacin Nijeriya mun samu matsaloli na wargajewar harkokin mu da lalacewar su da kuma matsala da mu ka samu da gwamnati wacce ta yi alƙawarin za ta tallafa mana ta gina mana harkokin mu, mu ka bada gudunmawar mu iya yin mu, amma har yanzu gwamnati ba ta waiwaye mu ba. Babu wani yunƙuri da su ka yi.

 “Don haka dole ta sa duk wanda ya ke meman cigaba, dole ya yunƙura ya fito daga Arewa a wannan harka tamu.

 “Kuma ina fatan abin da zan samu zai nunnunka abin da na ke samu a baya tun shiga ta harkar.” 

Zango ya bayyana cewa in har aka ƙara ganin sa a Arewa, to wani aiki na musamman aka gayyato shi ko kuma biki ya kawo shi. 

Ya yi kira ga al’ummar Arewa mazauna kudancin Nijeriya da su rungume shi da kyau, su riƙa gayyatar sa zuwa bukukuwa ko tarurrukan su domin ya nishaɗantar da su yadda ya kamata.

 “Yadda su ka san ni da jajircewa wajen bai wa jama’a nishaɗi, to ga nesa ta zo kusa, na zo kusa da su. Za su riƙa gani na a wasanni da bukukuwa.”

 Zango ya na da yaƙinin cewa kakar sa za ta yanke saƙa sosai a zaman sa na Kurmi, musamman ganin cewa “da ma a Kudu babu manyan jarumai ‘yan wasan Hausa.”

 Ya ce yanzu haka ya na kan aikin ƙulla dangantaka da wasu manyan mawaƙa biyar na Kudu, wato su Davido, Burna Boy, Tekno, Olamide da Lighter. Ya ce a wannan shekara mai shigowa ta 2020 za a ga bidiyoyin waƙoƙi da za su shirya shi da waɗannan mawaƙan.

 Amma dai ya sha alwashin cewa duk abin da zai yi a Legas, to zai kiyaye duk abin da zai taɓa mutuncin sa da na addinin sa. 

 Ya ƙara da cewa, “Kuma buri na shi ne ɗaga martabar harshen Hausa; don haka ne na zo in bunƙasa shi a nan Legas, in kuma ɗabbaka al’adar Bahaushe.”

 A ƙarshen hirar tasa da Aminiya, Adam A. Zango ya ragargaji abokan aikin sa na masana’antar finafinai ta Kannywood masu yi masa bi-ta-da-ƙulli, ya ce saboda su ne ma ya sa ya fice daga masana’antar.

 Ya ce: “Babu abin da ya rage a wannan masana’anta sai zalunci da sharri da cin mutunci a kai na. Ban ce a kan kowa ba.

 “Me ya sa za ka zauna a wajen mutanen da su ke cin mutuncin ka, su ke yi maka ƙazafi, su ke yi maka sharri, su ke neman lallai sai sun binne ka da ran ka? Wannan shi ne dalilin da ya sa na yanke hukuncin barin masana’antar Kannywood.”

Loading

Tags: Adam Zango
Previous Post

Haihuwa ta 5: Maryam Hiyana ta samu Nana Khadija

Next Post

Fati Ladan: Sirrin ɗorewar aure na tsawon shekara 6

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Fati Ladan da Shettima cikin farin ciki

Fati Ladan: Sirrin ɗorewar aure na tsawon shekara 6

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!