• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 11, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Batun Gwanja: In gaskiya ne, NBC ta soke soshiyal midiya mana – mawaƙi Ɗayyab Maiɗa’a

by DAGA ABBA MUHAMMAD
September 8, 2022
in Labarai
0
Ɗayyab Hassan (Maiɗa'a)

Ɗayyab Hassan (Maiɗa'a)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN mawaƙi a Kannywood, Ɗayyab Hassan, wanda aka fi sani da Maiɗa’a, ya ce idan da gaske Hukumar Kula Da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Nijeriya (Nigerian Broadcasting Corporation, NBC) ta ke yi, to ta dakatar da saka waƙoƙin Ado Gwanja a soshiyal midiya.

Ɗayyab ya yi waɗannan kalamai ne a lokacin da ya ke zantawa da mujallar Fim, bayan hukumar ta ba da umarnin dakatar da saka waƙar ‘Warr’ a gidajen rediyo da talbijin.

Mawaƙin ya ce, “Da ya ke hankali ya koma kan Ado Gwanja, wallahi wannan sam ba adalci aka yi wa kafafen yaɗa labarai ba, sai ma rainin wayo da ake nuna wa mutanen Arewa.”

Ya ci gaba da cewa, “Wallahi mawaƙan Turanci sun fi mu rashin mutunci da waƙoƙin su marasa ɗa’a.

“Idan ka duba, za ka ga suna da yawa. A nawa fahimtar, kawai ana so a nuna wa duniya cewa mu mawaƙan Arewa ba mu da tarbiyya ne. Kuma wannan al’amari kaf mutanen arewacin ƙasar nan zai shafa.

“Ni ba na goyon bayan Ado Gwanja na ke yi ba sam, amma ina aka kai mawaƙan (kudancin) Nijeriya marasa tarbiyya masu nuna tsiraici da nuna baɗala?

“Waɗannan waƙoƙi ana ganin cewa kamar ba za su ɓata mana tarbiyyar yara masu tasowa kamar ƙanne, ‘ya’ya da sauran su ba? Ko ana ganin ba za a riƙa motsa masu sha’awa ba ne?”

Ɗayyab Maiɗa’a ya ce, “Idan ka na mawaƙin Arewa, ba ka da galihu; duk abin da ka yi komai, ƙanƙantar sa, idan ya samu karɓuwa shi kenan ka zama mai lalata tarbiyya.

“Abin da ake tunanin Gwanja ya yi akwai ƙuruciya a cikin sa, ko kuma in ce akwai jahilci, ba ina nufin jahili ba ne, a’a, duk abin da ba ka da ilimin sa kai jahilin sa ne, in fa bai sani ɗin ba kenan.

“Wannan waƙa ta ‘Warr’ ko da an hana saka ta a gidajen talbijin da gidajen rediyo, to fa ta zama gwal a sana’ance, domin yanzu a TikTok, Instagram, Facebook, WatsApp da sauran su ake kallo yayin da komai ƙanƙantar waya za ta biya wa kowa buƙatun sa kowane iri.

“Idan gwamnatin Nijeriya ta na so ta burge, to ta rufe kafafen sada zumuntan na zamani, shi ne mafita, kuma shi ne zaman lafiya a kan dukkan makircin masu yaɗa farfaganda da sauran abin da ke kawo mana matsalolin rayuwa.”

Loading

Tags: Ado Gwanjadokamawaƙamawaƙan kuduNBCTarbiyya
Previous Post

Haramcin waƙa ta: Na yi gum, ba zan ce komai ba yanzu, inji Gwanja

Next Post

Zaɓen 2023: Fiye da mutane miliyan 3 za su yi zaɓe a sansanin ‘yan gudun hijira – INEC

Related Posts

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama
Labarai

Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama

August 2, 2026
Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11
Labarai

Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11

August 1, 2026
Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano
Labarai

Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano

July 15, 2026
Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu
Labarai

Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu

July 14, 2026
A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti
Labarai

A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti

July 9, 2026
Next Post

Zaɓen 2023: Fiye da mutane miliyan 3 za su yi zaɓe a sansanin 'yan gudun hijira - INEC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!