• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 1, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Samanja: Ga ni da rai na, ban mutu ba

by DAGA IRO MAMMAN
July 1, 2021
in Labarai
0
Cewar Samanja: Ga ni da rai na, ban mutu ba
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A YAU Alhamis aka wayi gari da labarin wai shahararren ɗan wasan kwaikwayo ɗin nan, Alhaji Usman Baba Pategi, wanda aka fi sani da suna Samanja Mazan Fama, ya rasu.

To amma mujallar Fim ta zanta da shi, inda ya ƙaryata labarin.

Labarin ya bazu a soshiyal midiya ne bayan wani tsohon darakta a Hukumar Talbijin ta Ƙasa (NTA) ya rubuta a shafin sa na Facebook cewa Allah ya yi wa Samanja rasuwa.

Nan da nan fitaccen ɗan jaridar nan Ibrahim Sheme ya sanar da wanda ya yi rubutun da kuma jama’a cewa Samanja dai na nan da ran shi.

Sheme ya ce a matsayin sa na wanda ke rubuta tarihin rayuwar Samanja shi da ma’aikacin gidan talbijin ɗin nan na KSTV da ke Kaduna, wato Sgafi’u Magaji Usman, ya na bada tabbacin cewa Samanja na nan da ran sa.

Sheme, wanda sanannen marubuci ne, ya ce sun yi magana da Samanja da iyalin sa jim kaɗan bayan sun karanta wannan labari da aka ƙaga a Facebook.

Ya ce bai kamata wanda ya ƙaga labarin ya tura irin wannan saƙo ba tare da ya tabbatar da ingancin sa ba.

Wanda ya fara bada labarin dai ya ɗauki gyara ba tare da ɓata lokaci ba, kuma ya goge rubutun nasa tare da bada haƙuri.

Samanja a lokacin da ya ke cikin ganiyar sa a shirin ‘Samanja Mazan Fama’ na gidan talbijin na NTA

Sai dai kash! labarin ya ci gaba da yaɗuwa a shafuka da guruf-guruf na soshiyal midiya.

Saboda haka ne dai abokin aikin Sheme, wato Shafi’u Magaji Usman, ya garzaya zuwa gidan Samanja da ke unguwar Kabala Costain a Kaduna, inda ya tattauna da tsohon ɗan wasan domin kawar da ji-ta-ji-tar.

A hirar tasu, Alhaji Usman Baba Pategi ya bayyana cewa shi dai ya na nan da ran sa bai mutu ba.

Ya ce, “Mutum da ran shi, ga shi ina magana ma da kai, ko ba haka ba ne? An taɓa ganin wanda ya mutu ya na magana da wani? Ba zai yiwu ba! Mutane ne dai kawai! Mutum ne kawai – ko mai son ka ne, ko maƙiyin ka ne!”

Samanja ya ce duk abin da Allah ya ƙaddara wa bawan sa, shi zai same shi.

Shi dai Alhaji Pategi, ya fara wasan kwaikwayo tun bayan dawowar sa daga Yaƙin Basasar Nijeriya, inda ya yi aikin soja, kuma ya ci gaba da gudanar da wasan ‘Samanja Mazan Fama’ da na ‘Duniya Budurwar Wawa’ har zuwa lokacin da ya yi ritaya saboda halin manyantaka da kuma rashin isasshiyar lafiya.

To Allah ta ba shi lafiya da ƙarin rayuwa mai albarka, amin.

Alhaji Usman Baba Pategi a lokacin hirar sa da Shafi’u Magaji Usman ɗazu da yamma

Loading

Tags: Duniya Budurwar Wawahausa actorsIbrahim ShemeKannywoodSamanjaSamanja Mazan FamaShafi'u Magaji UsmanUsman Baba Pategi
Previous Post

Zainab Booth ta rasu bayan tiyatar ƙwaƙwalwa

Next Post

Zai yi wahala a maye gurbin Zainab Booth – Jaruman Kannywood

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Zai yi wahala a maye gurbin Zainab Booth – Jaruman Kannywood

Zai yi wahala a maye gurbin Zainab Booth - Jaruman Kannywood

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!