• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Samanja: Ga ni da rai na, ban mutu ba

by DAGA IRO MAMMAN
July 1, 2021
in Labarai
0
Cewar Samanja: Ga ni da rai na, ban mutu ba
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A YAU Alhamis aka wayi gari da labarin wai shahararren ɗan wasan kwaikwayo ɗin nan, Alhaji Usman Baba Pategi, wanda aka fi sani da suna Samanja Mazan Fama, ya rasu.

To amma mujallar Fim ta zanta da shi, inda ya ƙaryata labarin.

Labarin ya bazu a soshiyal midiya ne bayan wani tsohon darakta a Hukumar Talbijin ta Ƙasa (NTA) ya rubuta a shafin sa na Facebook cewa Allah ya yi wa Samanja rasuwa.

Nan da nan fitaccen ɗan jaridar nan Ibrahim Sheme ya sanar da wanda ya yi rubutun da kuma jama’a cewa Samanja dai na nan da ran shi.

Sheme ya ce a matsayin sa na wanda ke rubuta tarihin rayuwar Samanja shi da ma’aikacin gidan talbijin ɗin nan na KSTV da ke Kaduna, wato Sgafi’u Magaji Usman, ya na bada tabbacin cewa Samanja na nan da ran sa.

Sheme, wanda sanannen marubuci ne, ya ce sun yi magana da Samanja da iyalin sa jim kaɗan bayan sun karanta wannan labari da aka ƙaga a Facebook.

Ya ce bai kamata wanda ya ƙaga labarin ya tura irin wannan saƙo ba tare da ya tabbatar da ingancin sa ba.

Wanda ya fara bada labarin dai ya ɗauki gyara ba tare da ɓata lokaci ba, kuma ya goge rubutun nasa tare da bada haƙuri.

Samanja a lokacin da ya ke cikin ganiyar sa a shirin ‘Samanja Mazan Fama’ na gidan talbijin na NTA

Sai dai kash! labarin ya ci gaba da yaɗuwa a shafuka da guruf-guruf na soshiyal midiya.

Saboda haka ne dai abokin aikin Sheme, wato Shafi’u Magaji Usman, ya garzaya zuwa gidan Samanja da ke unguwar Kabala Costain a Kaduna, inda ya tattauna da tsohon ɗan wasan domin kawar da ji-ta-ji-tar.

A hirar tasu, Alhaji Usman Baba Pategi ya bayyana cewa shi dai ya na nan da ran sa bai mutu ba.

Ya ce, “Mutum da ran shi, ga shi ina magana ma da kai, ko ba haka ba ne? An taɓa ganin wanda ya mutu ya na magana da wani? Ba zai yiwu ba! Mutane ne dai kawai! Mutum ne kawai – ko mai son ka ne, ko maƙiyin ka ne!”

Samanja ya ce duk abin da Allah ya ƙaddara wa bawan sa, shi zai same shi.

Shi dai Alhaji Pategi, ya fara wasan kwaikwayo tun bayan dawowar sa daga Yaƙin Basasar Nijeriya, inda ya yi aikin soja, kuma ya ci gaba da gudanar da wasan ‘Samanja Mazan Fama’ da na ‘Duniya Budurwar Wawa’ har zuwa lokacin da ya yi ritaya saboda halin manyantaka da kuma rashin isasshiyar lafiya.

To Allah ta ba shi lafiya da ƙarin rayuwa mai albarka, amin.

Alhaji Usman Baba Pategi a lokacin hirar sa da Shafi’u Magaji Usman ɗazu da yamma

Loading

Tags: Duniya Budurwar Wawahausa actorsIbrahim ShemeKannywoodSamanjaSamanja Mazan FamaShafi'u Magaji UsmanUsman Baba Pategi
Previous Post

Zainab Booth ta rasu bayan tiyatar ƙwaƙwalwa

Next Post

Zai yi wahala a maye gurbin Zainab Booth – Jaruman Kannywood

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Zai yi wahala a maye gurbin Zainab Booth – Jaruman Kannywood

Zai yi wahala a maye gurbin Zainab Booth - Jaruman Kannywood

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!