DAƊI biyu ya lulluɓe marubuciya Bilkisu Yusuf Ali a wannan makon, yayin da ta samun jika, sannan kuma ta samu digiri na uku wanda ake kira digirin digirgir ko dakta.
Kamar yau ne aka yi bikin ‘yar Malama Bilkisu ɗin, wato Sarra Tasi’u Ya’u Babura. Bisa yardar Allah a shekara guda da yin auren sai ga shi Allah ya albarkaci auren da ƙaruwa.
A ranar Talata, 10 ga Disamba, 2024 Sarra ta haifi ɗa namiji, wanda aka raɗa wa sunan Muhammad Tasi’u Salihu, wato sunan mahaifin ta.


A ranar Laraba aka yi bikin raɗin sunan a gidan mahaifin jaririn da ke Tudun Yola a cikin garin Kano.
‘Yan’uwa da abokan arziki sun halarta domin taya murna.


Mahalartan sun haɗa da rubuta irin su Sadiya Garba Yakasai, Lubabatu Ya’u, Hadiza Nuhu Gudaji, Bushira Nakura, Asma’u Sani, Hauwa Lawan Maiturare, Fauziyya D. Sulaiman, Halima Kurmin Mashi, da Fadila Aliyu.
A jiya kuma Bilkisu, wadda Malama ce a Jami’ar Alqalam da ke Katsina, ta kare kundin bincike da ta yi na zama dakta.
An yi zaman ne a Jami’ar Umaru Musa Yar’adua (UMYU) da ke Katsina, inda a nan ne ta yi karatun ta na digiri na uku.


Bayan an tabbatar mata da nasara a zaman, sai Dakta Bilkisu ta hau Facebook inda ta bayyana farin cikin ta, har tana tunawa da yadda mahaifin ta, marigayi Dakta Yusuf Ali, zai ji inda yana raye ta samu wannan gagarumar nasara.
Ta ce: “Allan ne kaɗai ya san irin farin cikin da Malam zai yi a yau da yana raye.”
Ta ƙara da cewa: “A yau, Malam na cika ma burin ka na kammala Ph.D (digiri na uku) cikin nasara a ɓangaren Adabi daga Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya a Jami’ar Umaru Musa Yar’adua, Katsina.
“A ci gaba da hutawa, Imamu na; muna tare da kai da duk abin da kake so.
Dr. Bilkisu Yusuf Ali.”
Wannan muhimmin zango ne Hajiya Bilkisu ta kai, domin kuwa ta ɗan jima tana wannan karatu na zama dakta, har wasu na hangen ƙila ba za ta kai labari ba.
Ɗimbin jama’a sun taya ta murnar wannan sabon matsayi da ta samu a fagen ilimi.