ALLAH ya azurta ɗaya daga cikin manyan daraktocin finafinan Hausa da ke Jamhuriyar Nijar, Bassirou Garba Sarkin Fulani, da samun ƙaruwar ‘ya mace.
Maiɗakin sa ta haifi jaririyar da misalin ƙarfe 4:40 na yamma a ranar Talata, 18 ga Afrilu, 2023 a gidan sa da ke birnin Maraɗi a Jamhuriyar Nijar.
Daraktan ya bayyana wa mujallar Fim farin cikin sa da godiyar sa ga Allah da samun wannan haihuwar, ya ce: “Alhamdu lillah, Allah ya ba mu ƙaruwar ‘ya mace wadda za ta karɓi sunan Iklas. Mu na barar addu’a domin neman yardar Allah don ta kasance mai yin hidima ga al’ummar Musulmi da Musulunci”.
Kaɗan daga cikin finafinan da Bassirou Garba ya bayar da umarni su ne ‘Jagwal’, Ummaru’, ‘Ajalin Ka’, ‘Zama Ɗaya’, ‘Ruwan Dare’, ‘Arabi Da Boko’, ‘Amal’, ‘Iman’, da kuma ‘Igiyar Ƙasa’.
![]()







