• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Furodusan Kannywood Abdul Isma’il Musa ya zama shugaban MOPPAN ta Sokoto

by DAGA ABBA MUHAMMAD
December 12, 2022
in Labarai
0
Ana rantsar da sababbin shugabannin

Ana rantsar da sababbin shugabannin

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

‘YA’YAN Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), reshen Jihar Sokoto, ta zaɓi Malam Abdul Isma’il Musa a matsayin shugabannin su.

A yau Lahadi, 12 ga Disamba, 2022 aka gudanar da zaɓen sababbin shugabannin ƙungiyar a ɗakin taro na Ƙaramar Hukumar Sokoto ta Kudu, a Jihar Sokoto.

Da farko an fara da tantance wakilai, waɗanda za su kaɗa ƙuri’a, daga misalin ƙarfe 10:00 na safe har zuwa ƙarfe 12:00 na rana.

Sabon Ciyaman, Abdul Isma’il Musa

Daga nan kuma, da misalin ƙarfe 12:30, aka fara kaɗa ƙuri’a. Bayan an kammala, sai aka faɗi sakamakon zaɓe. 

Bayan an yi sallar azahar an dawo, sai aka rantsar da waɗanda su ka samu nasara. 

An rantsar da su da misalin ƙarfe 2:30 na rana, sannan aka ba kowanne su satifiket, shaidar kama aiki.

Waɗanda su ka samu nasarar lashe zaɓen su ne: Abdul Isma’il Musa a matsayin Ciyaman; Shehu Ɗantuni Shagari, Mataimakin Ciyaman; Hajiya Halima Muhammad Baba, Sakatare; Bashiru Abdullahi Ejo, Mataimakin Sakatare, da Bala Ibrahim Kware, Ma’aji.

Sauran su ne Alhaji Sule Jibril, Sakataren Kuɗi; Murtala Hassan, Jami’in Hulɗa da Jama’a na 1; Yusuf S.Yaƙi, Jami’in Hulɗa da Jama’a na 2; Shafa’aru Sani, Jam’in Walwala; Abubakar Alhaji, Sakataren Tsare-tsare; Ɗahiru Muktar, Mai Binciken Kuɗi na 1, da Rabi’a Isa, Mai Binciken Kuɗi ta 2.

Da ya ke zantawa da mujallar Fim, wakilin uwar ƙungiyar ta ƙasa, kuma mai bincken kuɗi na biyu na ƙungiyar ta ƙasa, Malam Bello Achida, ya ce, “Ina godiya ga Allah da ya sa aka yi wannan zaɓen lafiya, kuma ina kira ga sababbin shugabanni da su yi wa mambobin su adalci, kuma su janyo waɗanda ba su yi nasara ba su tafi tare.”

Lokacin rantsar da sababbin shugabannin
Daga hagu: Lawal Rabe Lemu, wakilin shugaban MOPPAN na ƙasa a wurin zaɓe, kuma mai kai sakamakon zaɓen (returning officer), da Malam Bello Achida ya na jawabi

Loading

Tags: Abdul Isma'il MusaBello AchidafurodusoshiMOPPANrantsarwashugabannisokotozaɓe
Previous Post

Adam A. Zango ga ‘yan fim: Ba mu da mafita sai mu gyara halayen mu marasa kyau

Next Post

An karrama masu harkar nishaɗantarwa a taron Makon Nishaɗantarwa na Arewa

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Shugaban MOPPAN, Dakta Ahmad Sarari (a dama), ya na karɓar kyautar karramawar sa a taron

An karrama masu harkar nishaɗantarwa a taron Makon Nishaɗantarwa na Arewa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!