• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Kano ta tsaida shirin ‘Kwana Casa’in’ da na ‘Gidan Badamasi’

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
April 7, 2020
in Labarai
0
Fostar 'Kwana Casa'in', zango na uku ... wanda aka fara ran Lahadi

Fostar 'Kwana Casa'in', zango na uku ... wanda aka fara ran Lahadi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
GWAMNATIN Jihar Kano ta umarci tashar talbijin ɗin nan mai farin jini ta Arewa24 da ta dakatar da nuna wasu shirye-shiryen dirama masu dogon zango guda biyu da ta ke nunawa, wato ‘Gidan Badamasi’ da kuma ‘Kwana Casa’in’.
 
Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta jihar ce ta aika wa gidan talbijin ɗin da umarnin a cikin wata takarda mai ɗauke da kwanan wata 7/4/2020.
 
Shugaban hukumar, Alhaji Isma’il Na’abba (Afakallah), shi ne ya rattana hannu a kan takardar.
 
Dakatar da waɗannan finafinan ya faru ne saboda hukumar ta ce ba ta duba su ba ake haska su.
 
Hukumar ta ce ƙin ba ta wasannin domin ta tace su ya saɓa wa dokar ta.
 
Ta nemi a dakatar da haska su har zuwa lokacin da aka cika ƙa’idar ta.
 
Su dai waɗannan finafinai biyu, su na da ɗimbin masu kallon su a duk faɗin duniya saboda tasirin su ga masu kallo. 
 
A yanzu babu wani wasan talbijin da ake kallo a arewacin Nijeriya da duk inda ake jin Hausa kamar su. 
 
A cikin wannan satin ne aka shiga zango na biyu na shirin ‘Kwana Casa’in’, to amma tun da aka fara nuna shi jama’a su ka fara yin ƙorafi dangane da yadda salon sa ya canza.
Takardar da Hukumar Tace Finafinai ta tura wa Arewa24
Mujallar Fim ta fahimci cewa da man ko a can baya ana ganin kamar shirin ya na tona asirin gwamnati ne, don haka ake ganin babu mamaki idan gwamnatin Kano ta yi amfani da hukumar tace finafinan domin a dakatar da shi. 
 
Mujallar Fim ta tuntuɓi wani jami’in Arewa24 ya furta wani abu a kan wannan abu da ya faru, sai ya ce ba hurumin sa ba ne amma hukumar gidan ce za ta ce wani abu.
 
Ya zuwa lokacin wallafa wannan labari dai hukumar gidan talbijin ɗin ba ta ce komai ba dangane da wannan dokar da aka ƙaƙaba mata.
 
Abin da jama’a su ka zuba ido su gani shi ne yadda wannan doka za ta yi tasiri a kan gidan talbijin ɗin, wanda ake ganin kamar ya fi ƙarfin Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano.

Loading

Previous Post

Illar ƙunzugu da tsumma, daga Hadiza Nuhu Gudaji

Next Post

Baba Ari ya samu tagwaye

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Baba Ari, murmushi har kunne, tare da tagwayen sa da wani yayan su

Baba Ari ya samu tagwaye

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!