* Ƙungiyar su ta samu rajistar tarayya
ƘUNGIYAR jaruman finafinan Hausa ta ƙasa, wato ‘Nigerian Guild of Artistes Hausa Language’, ta jaddada goyon bayan ta ga shugaban Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Malam Isma’il Na’abba (Afakallahu).
Jaruman sun yi haka ne a lokacin da su kai ziyara ga shugaban domin gabatar masa da rajistar ƙungiyar da ta samu daga Gwamnatin Tarayya, wanda ya zamar da ita a matsayin halastacciyar ƙungiya.
A safiyar Alhamis, 5 ga Maris, 2020 tawagar ƙungiyar a ƙarƙashin shugabancin Alhassan Kwalle, su ka je ofishin hukumar domin wannan ziyarar.
A lokacin da ya ke bayyana dalilin zuwan nasu, Alhassan Kwalle ya bayyana cewa manufar zuwan nasu shi ne domin su kai ziyarar ban-girma ga shugaban hukumar saboda namijin ƙoƙarin da ya ke yi wajen kawo gyara a cikin masana’antar ta finafinan Hausa, su ka ce don haka ne su ka je domin su yaba masa.

Ya ƙara da cewa “A ɓangare guda kuma wannan ziyarar tamu, mun zo da takardar rajistar ƙungiyar ta C.A.C. wadda mu ka samu, kuma hakan ya zamar da ita halastacciyar ƙungiyar da gwamnatin Nijeriya ta san da zaman ta.
“Don haka ne mu ka zo da wannan takarda ta rajista da mu ka samu domin shugaban Hukumar Tace Finafinai ta Kano ya sanya mata albarka.
“Don haka mu na addu’ar Allah ya ƙara jagoranci da kuma bada ƙarfin gwiwar yi wa jama’a hidima”.
Shi ma da ya ke nasa jawabin, Afakallahu ya nuna farin cikin sa da ziyarar, ya ce hakan ya nuna cewar su masu biyayya ga shugabanci ne.
Saboda haka ya yi kira a gare su da su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya domin cigaba da tsare-tsare kan manufofin da ta ke da shi na alheri ga masana’antar finafinai ta Kannywood.
Daga ƙarshe, ya yi fatan samun nasara ga ƙungiyar bisa manufofin da ta sanya a gaba.
![]()







