JARUMIN barkwanci a Kannywood, Ibrahim Abubakar Ibrahim, wanda aka fi sani da Yamu Baba, ya yi bankwana da kwanan shago a jiya Asabar.
An ɗaura auren sa da sahibar sa, Hauwa’u Musa Abubakar, da misalin ƙarfe 11:00 na safe a gidan Alhaji Ibrahim Mai Taya da ke Layin Ɗanmaraya, a Jos, Jihar Filato, a kan sadaki N300,000.

Waɗanda su ka halarci ɗaurin auren sun haɗa da Nazifi Zuma, S. Nigger, Kina Gombe, Abdul Zero, Abdul D. One, Sabon Oji, Sadiq Sani Sadiq, Sani Ahmad, Kawu Ɗan Sarki, Ɗan Musa Gombe, Umar Big Show da Mubson Zamani.

Kafin ranar bikin an gudanar da shagulgula kamar haka:
- Talata, 23 ga Afrilu – Ƙwallon ƙafa a tsakanin ‘yan Kannywood da ‘yan ƙwallon Plateau United.
- Laraba, 24 ga Afrilu – Ranar Hausawa a tsohon Gidan Zu.
- Alhamis, 25 ga Afrilu – Yaumul Rasul.
- Juma’a 26 ga Afrilu – Bikin Ranar Jarumai (Artistes Day) a Plateau Hotel.
Bayan an ɗaura auren, an yi ƙasaitaccen dina da misalin ƙarfe 7:00 na dare a Lamonde Hotel, Jos.
Mata ‘yan fim da su ka halarci bukukuwan da aka yi sun haɗa da Jamila Nagudu, Momee Gombe, Suhailat Ishaq, Asma’u Wakili, Khadija Muhammad, Amina ‘Yar Fillo, Ummulkhairi, Teema Yola, Safiya ‘Yar Ghana, Zainab Sambisa, Safiya Macijiya, Hafsat Bauchi da Asmy Kogin Zuma.

Aminin ango, Tynking Mai Gashi, ya yi wa dukkan waɗanda su ka halarci bikin godiya da ban-gajiya, inda ya ce, “Amincin Allah ya tabbata ga duk al’ummar Manzon Allah (s.a.w).
“Da farko ina miƙa saƙon gaisuwa ga duk jama’ar da su ka samu damar zuwa taron bikin abokin mu Yamu Baba. Mu na godiya matuƙa kuma mu na wa kowa fatan alkhairi a cikin rayuwar sa.

“Sannan kuma mu na yi wa kowa fatan komawa gida cikin ƙoshin lafiya da kwanciyar hankali kamar yadda kowa ya zo cikin ƙoshin lafiya da farin ciki.
“Tabbas godiya ita ce kawai abin da za mu iya saka wa masoyan mu da kuma iyayen mu da su ka ba da gudunmawa wajen ba mu tarbiyya da duk wata dama domin inganta rayuwar mu da kuma tabbatar da farin ciki a rayuwar mu.

“Kuma don girman Allah idan akwai wanda aka yi wa ba daidai ba ko kuma ya ji kamar an yi masa rashin adalci, mu na masu ba wa kowa haƙuri kuma mu na masu neman afuwa da yafiyar kowa da kowa. Allah ya sa mu dace duniya da lahira baki ɗaya, amin.”
