• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mahaifin jaruma Aisha Muhammad ya kwanta dama

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
July 10, 2021
in Labarai
0
Mahaifin jaruma Aisha Muhammad ya kwanta dama
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAH ya yi wa mahaifin fitacciyar jarumar Kannywood Aisha Muhammad Adam rasuwa.

Malam Muhammad Adamu ya rasu ne a safiyar yau Asabar a asibiti a Kano bayan ya sha fama da rashin lafiya.

Shekarun sa 86 a duniya.

Marigayin dai ɗan asalin Jihar Adamawa ne wanda ya dawo unguwar Sabuwar Gandu, Kano, da zama a shekarun baya. 

An gudanar da jana’izar sa kamar yadda Musulunci ya tanada, aka kai shi maƙabartar da ke Kwanar Barka, Sabuwar Gandu, da misalin ƙarfe 1 na rana.

Aisha Muhammad, wadda ita ce babbar ‘yar marigayin, ta shaida wa mujallar Fim cewa mahaifin ta ya bar ‘ya’ya takwas, maza 4 mata 4, da kuma matar sa ɗaya.

Ta ƙara da cewa ta ƙadu matuƙa saboda rashin mahaifin nata wanda da man shi kaɗai ya rage mata bayan rasuwar mahaifiyar ta.

Ta ce, “Babu abin da zan ce da Allah sai godiya, domin ina gida aka kira ni aka ce ya faɗi kamar yadda matar sa ta sanar da ni yau da asuba, kuma da man na san ya na da lalura. 

Malam Muhammad Adamu ya rasu ya na da shekara 86 a duniya.

“Nan da nan na zo mu ka kai shi asibiti, har ta kai ga an sa masa abin shaƙar iska (oxygen). Ana haka kuma Allah ya yi masa cikawa.

“Da man shi Allah da ya halicce mu mu ka zo duniya dole zai jarabce mu, amma na ji ɗaci domin yau na rasa kowa, ɗan idon da na ke gani ba ni da shi. Ba ni da kowa, ba ni da uwa ba ni da uba. Allah ya jiƙan su da rahama.” Da faɗin haka sai ta soma kuka.

Tuni dai abokan sana’ar Aisha na fim su ka fara aika mata da saƙon ta’aziyya, yayin da wasu su ka je har gida su ka yi mata gaisuwa.

Allah ya jiƙan Malam Muhammadu, ya ba iyalan sa jimirin jure wannan babban rashi, amin.

Cewar Aisha a cikin alhini: “Yau na rasa kowa, ɗan idon da na ke gani ba ni da shi. Ba ni da kowa, ba ni da uwa ba ni da uba.”

Loading

Previous Post

Hoto: Alhinin Amude Booth a gaban kabarin mamar shi

Next Post

Hotuna: ‘Yan fim sun yi taron addu’a ga Zainab Booth

Related Posts

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry
Labarai

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
Next Post
Hotuna: ‘Yan fim sun yi taron addu’a ga Zainab Booth

Hotuna: 'Yan fim sun yi taron addu'a ga Zainab Booth

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!