• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, May 18, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mahaifin jaruma Aisha Muhammad ya kwanta dama

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
July 10, 2021
in Labarai
0
Mahaifin jaruma Aisha Muhammad ya kwanta dama
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAH ya yi wa mahaifin fitacciyar jarumar Kannywood Aisha Muhammad Adam rasuwa.

Malam Muhammad Adamu ya rasu ne a safiyar yau Asabar a asibiti a Kano bayan ya sha fama da rashin lafiya.

Shekarun sa 86 a duniya.

Marigayin dai ɗan asalin Jihar Adamawa ne wanda ya dawo unguwar Sabuwar Gandu, Kano, da zama a shekarun baya. 

An gudanar da jana’izar sa kamar yadda Musulunci ya tanada, aka kai shi maƙabartar da ke Kwanar Barka, Sabuwar Gandu, da misalin ƙarfe 1 na rana.

Aisha Muhammad, wadda ita ce babbar ‘yar marigayin, ta shaida wa mujallar Fim cewa mahaifin ta ya bar ‘ya’ya takwas, maza 4 mata 4, da kuma matar sa ɗaya.

Ta ƙara da cewa ta ƙadu matuƙa saboda rashin mahaifin nata wanda da man shi kaɗai ya rage mata bayan rasuwar mahaifiyar ta.

Ta ce, “Babu abin da zan ce da Allah sai godiya, domin ina gida aka kira ni aka ce ya faɗi kamar yadda matar sa ta sanar da ni yau da asuba, kuma da man na san ya na da lalura. 

Malam Muhammad Adamu ya rasu ya na da shekara 86 a duniya.

“Nan da nan na zo mu ka kai shi asibiti, har ta kai ga an sa masa abin shaƙar iska (oxygen). Ana haka kuma Allah ya yi masa cikawa.

“Da man shi Allah da ya halicce mu mu ka zo duniya dole zai jarabce mu, amma na ji ɗaci domin yau na rasa kowa, ɗan idon da na ke gani ba ni da shi. Ba ni da kowa, ba ni da uwa ba ni da uba. Allah ya jiƙan su da rahama.” Da faɗin haka sai ta soma kuka.

Tuni dai abokan sana’ar Aisha na fim su ka fara aika mata da saƙon ta’aziyya, yayin da wasu su ka je har gida su ka yi mata gaisuwa.

Allah ya jiƙan Malam Muhammadu, ya ba iyalan sa jimirin jure wannan babban rashi, amin.

Cewar Aisha a cikin alhini: “Yau na rasa kowa, ɗan idon da na ke gani ba ni da shi. Ba ni da kowa, ba ni da uwa ba ni da uba.”

Loading

Previous Post

Hoto: Alhinin Amude Booth a gaban kabarin mamar shi

Next Post

Hotuna: ‘Yan fim sun yi taron addu’a ga Zainab Booth

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Hotuna: ‘Yan fim sun yi taron addu’a ga Zainab Booth

Hotuna: 'Yan fim sun yi taron addu'a ga Zainab Booth

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!